ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin A Watannin Farkon Bana Zai Kara Karfafa Gwiwa A Duniya

by CGTN Hausa
2 years ago
arziki

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

A baya-bayan nan, sassan gwamnatin kasar Sin sun fitar da alkaluma game da ma’aunan tattalin arziki 3 da suka hada da na yawan kayayyakin da masana’antu ke sayarwa, da na bangaren kasuwanci da bai shafi samar da kayayyaki ba, da kuma na samarwa da fitar da kayayyakin, wadanda suka karu da kaso 1.7 da 1.6 da 1.8 idan aka kwatanta da makamancin lokacin a bara.

Na tuna yadda a lokacin da gwamnatin kasar Sin ta gabatar da rahoton aiki da bayyana burinta na samun karuwar tattalin arziki da kaso 5 a bana, na ji da kunnena wasu kafafen yada labaran yammacin duniya na cewa, kasar Sin ba ta bayyana yadda za a yi ta samu wannan ci gaba ba. Wato kamar su na ganin wannan burin ba mai yuwuwa ba ne. Amma wadannan alkaluma da aka gabatar sun nuna cewa, kasar Sin ta san abun da take yi kuma ta na da yakinin cimma burikan da ta sanya a gaba. A matsayin wadda ta shafe shekaru a kasar Sin, na san kasar ba ta sanya burin da ba za ta iya cimmawa ba, ko in ce, ban ma taba ganin ta sanya wani buri da ta gagara cimmawa ba.

  • Sin Da Faransa Sun Amince Da Gina Alaka Bisa Daidaito Da Hangen Nesa 

Ci gaban da Sin ta samu cikin wadannan watanni, bai tsaya kadai ga wadannan ma’aunai 3 ba, an kuma samu bunkasar wasu manyan fannoni kamar na samar da hidimomi da rayuwar al’umma da sayyaya da sauransu. Abun da irin wadancan kafofin watsa labarai da na bayyana a baya ba su gane ba shi ne, tattalin arzikin kasar Sin na bisa tubali mai kwari dake da juriya. Haka kuma, kasar ba ta dogara da kasashen waje wajen raya tattalin arzikinta ba, domin kasar Sin ta mayar da hankali ne wajen amfani da albarkatun da ta mallaka a cikin gida da kyawawan dabarun da suka dace da ita, da kuma fasahohi da karfinta na kirkire-kirkire. Misali, a cikin bangarorin da suka samu ci gaba, akwai rayuwar al’umma da karuwar sayayya a cikin gida. Kyautatuwar rayuwar al’umma na nufin samun kwanciyar hankali da biyan bukatu da kuma samuwar wadata. Samuwar wadata kuma shi ne ke kara ingiza sayyaya da kashe kudi a cikin gida, wanda ke bayar da gudunmuwa ga tattalin arziki. A ganina, wadannan ci gaba da aka samu cikin kankanin lokaci, somin tabi ne na irin ci gaban da za a kai ga cimmawa zuwa karshen shekara. Haka kuma, ba kasar Sin kadai za ta amfana ba, domin wannan sakamako da aka samu a lokaci kalilan, ba karfafa gwiwar duniya kadai zai yi ba, har ma da samar da makoma mai haske ga tattalin arzikin duniya kamar yadda ya saba.

ADVERTISEMENT
arziki
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

MASU ALAKA

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya
Daga Birnin Sin

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Next Post
An Gano Dajin Da Ya Fi Shekara Miliyan Hudu A Duniya

An Gano Dajin Da Ya Fi Shekara Miliyan Hudu A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.