• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cibiyar Binciken Harkar Noma (IAR) Ta Samar Da Irin Masara Mai Inganci

by Idris Umar
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Cibiyar binciken harkar noma ta Jami’ar Ahamadu Bello da ke Zariya (IAR), ta yi taron gani da ido na fitar da Irin Masara mafi inganci ga manoman wannan kasa baki-daya.

Daya daga cikin wadanda suka jagoraci wannan bincike, Farfesa Rabi’u ya bayyana cibiyar binciken harhar nomar wato, ‘Institute of Agriculture Research’ a matsayin wadda ta fitar da ranar 12 ga watan Satumbar shekarar 2023, domin shaida wa duniya shirinta na ‘TELA MAIZE’, ma’ana rana ta musamman don nuna wa kasarmu da manoman duniya Irin Masara mai suna ‘TELA’, wacce take dauke da sinadarai masu yawan gaske.

  • Duk Da Tazarar Dake Tsakaninmu, Za Mu Iya Jin Dadin Kyakkyawar Wata Tare 
  • Duk Da Tazarar Dake Tsakaninmu, Za Mu Iya Jin Dadin Kyakkyawar Wata Tare 

Ya ce, dalilin gudanar da wannan taro a wannan gona shi ne, domin manoma su shaida banbancin da ke tsakanin sabon Irin ‘TELA MAIZE’, da kuma saura Irin da ake da su a halin yanzu.

Farfesan ya kara da cewa, a wannan gona ana shuka masara kala daban-daban, don tantance abin da cibiyar ke son jama’a su shaida tsakanin sauran Irin masarar da sabo na ‘TELA  MAIZE’.

A kalla manoma daga cibiyoyi da kungiyoyi daban-daban sun gamsu da wannan sabon Iri da wannan cibiya ta kirkiro a zamanace tare da yin jinjina ga wannan nazari na bincike da aka gudanar.

Shi ma a nasa tsokacin, Shugaban Cibiyar Farfesa M.F Ishiyaku, ya ce, “Da farko ina godiya a madadin ‘Institute for Agricultural Research’ ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Samaru Zariya, wadda  ke jin dadin kula da daukar nauyi daga Ma’aikatan Aikin Gona ta tarayya, ina yi muku barka da zuwa wannan hamshakin taro na gani da ido. Ina kuma mika godiyata ta musamman, ga manoma, musamman wadanda suka tari aradu da ka suke karbar fasahohinmu na gwaji, domin tarar aradu da ka ne ka karbi abin da ba ka san ingancinsa ba, saboda ka ba da gaskiya ka jarraba shi, domin ta hanyar ka wani dan’uwanka ma zai gani ya assasa wannan abin, shi ya sa har kullum bincikenmu ba ya cika har sai mun shigo da manoma ciki sun sa mana hannu kafin ya samu karbuwa.”

Saboda haka, ya kamata manoma mu fahimta cewa wannan daya  daga cikin yunkurin da Gwamnatin Tarayya ke yi na rage matsalolin noma a wannan kasa. Daya daga cikin matsalar da manomi ke fuskanta ita ce, matsalar hauhawar farashi ta yadda zai zuba jari a harkarsa ta noma har ya ci riba.

Sa’annan, shugaban kungiyar binciken ya yi bayani dangane da yadda wata tsutsa da ake kira da cema ‘Fall Army Worm’, wadda manoman masara a ‘yan shekarun nan muka wayi gari Allah ya jefo mana ita, wanda idan ba a yi sa’a ba sai ka

wayi gari ka ga gonarka da take da yabanya mai kyau, ana sa rai za a samu abin kirki sai ka ga duk daga zuciyarta ta lalace an yi asarar ta baki-daya.

Har ila yau, babban makasudin wannan taro shi ne, tabbatar wa manoma cewa, tana iya yiwuwa a bullo da ingantaccen Iri na masara, wanda zai jure kansa ba tare da an yi masa feshin

magani ba, ma’ana zai iya jure kansa da kansa. Mun gamsu wannan sabon Iri yana da wannan inganci kwarai da gaske, amma mun zo ne domin mu sake jaddada wannan.

Saboda haka, na ke kara jinjina wa manoman da suka yi fice wajen rungumar sababbin fasahohi ba wannan kawai ba, har ma sauran fasahohi na shekarun baya da muka yi ta yi. Idan za ku iya tunawa, wannan cibiya tamu a wannan shekare ne ta cika shekaru dari da daya cif. A wannan zamani na wannan cibiya tamu, mu muka dauki alhakin yada dukkannin wani ingantaccen aikin noma, kama daga rainon ‘ya’yan itatuwa, hatsi, dawa, gero, masara, wake, waken suya da sauran makamantansu har ya zuwa yanzu din nan, kafin a da aka yi garambawul ga irin nauye-nauyen da aka dora mana a sanadiyar sake kirkiro da wasu cibiyoyin binciken aka dan rage mana nauyi.

Akwai wadanda babu abin da ya hada su da noma, amma ganin irin fa’idar da ake samu a cikinsa ya sa suka yi cincirindo suka

rungume shi, saboda haka ina ga mu wadanda muka gaje shi a matsayin sana’a. Babu shakka, noma yana ba wa ‘yan Nijeriya kusan kashi 66 cikin 100, wanda ya yi daidai da kimanin kusan mutum miliyan 160 aikin yi. Saboda haka, duk wani manomi

da ya samu karuwar tattalin arziki, daidai ya ke da kamar ka dauki wani ma’aikaci aiki ka rika biyan sa albashi duk shekara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kungiyoyin CONESAM Sun Baje Kolin Fasahar Sarrafa Kayan Amfanin Gona

Next Post

Bikin Kafuwar Daular Saudiyya Shekara 93: Abubuwan Da Ya Kamata A Sani

Related

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

9 hours ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

16 hours ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Next Post
Bikin Kafuwar Daular Saudiyya Shekara 93: Abubuwan Da Ya Kamata A Sani

Bikin Kafuwar Daular Saudiyya Shekara 93: Abubuwan Da Ya Kamata A Sani

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.