• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cibiyar Binciken Harkar Noma (IAR) Ta Samar Da Irin Masara Mai Inganci

by Idris Umar
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Cibiyar binciken harkar noma ta Jami’ar Ahamadu Bello da ke Zariya (IAR), ta yi taron gani da ido na fitar da Irin Masara mafi inganci ga manoman wannan kasa baki-daya.

Daya daga cikin wadanda suka jagoraci wannan bincike, Farfesa Rabi’u ya bayyana cibiyar binciken harhar nomar wato, ‘Institute of Agriculture Research’ a matsayin wadda ta fitar da ranar 12 ga watan Satumbar shekarar 2023, domin shaida wa duniya shirinta na ‘TELA MAIZE’, ma’ana rana ta musamman don nuna wa kasarmu da manoman duniya Irin Masara mai suna ‘TELA’, wacce take dauke da sinadarai masu yawan gaske.

  • Duk Da Tazarar Dake Tsakaninmu, Za Mu Iya Jin Dadin Kyakkyawar Wata Tare 
  • Duk Da Tazarar Dake Tsakaninmu, Za Mu Iya Jin Dadin Kyakkyawar Wata Tare 

Ya ce, dalilin gudanar da wannan taro a wannan gona shi ne, domin manoma su shaida banbancin da ke tsakanin sabon Irin ‘TELA MAIZE’, da kuma saura Irin da ake da su a halin yanzu.

Farfesan ya kara da cewa, a wannan gona ana shuka masara kala daban-daban, don tantance abin da cibiyar ke son jama’a su shaida tsakanin sauran Irin masarar da sabo na ‘TELA  MAIZE’.

A kalla manoma daga cibiyoyi da kungiyoyi daban-daban sun gamsu da wannan sabon Iri da wannan cibiya ta kirkiro a zamanace tare da yin jinjina ga wannan nazari na bincike da aka gudanar.

Shi ma a nasa tsokacin, Shugaban Cibiyar Farfesa M.F Ishiyaku, ya ce, “Da farko ina godiya a madadin ‘Institute for Agricultural Research’ ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Samaru Zariya, wadda  ke jin dadin kula da daukar nauyi daga Ma’aikatan Aikin Gona ta tarayya, ina yi muku barka da zuwa wannan hamshakin taro na gani da ido. Ina kuma mika godiyata ta musamman, ga manoma, musamman wadanda suka tari aradu da ka suke karbar fasahohinmu na gwaji, domin tarar aradu da ka ne ka karbi abin da ba ka san ingancinsa ba, saboda ka ba da gaskiya ka jarraba shi, domin ta hanyar ka wani dan’uwanka ma zai gani ya assasa wannan abin, shi ya sa har kullum bincikenmu ba ya cika har sai mun shigo da manoma ciki sun sa mana hannu kafin ya samu karbuwa.”

Saboda haka, ya kamata manoma mu fahimta cewa wannan daya  daga cikin yunkurin da Gwamnatin Tarayya ke yi na rage matsalolin noma a wannan kasa. Daya daga cikin matsalar da manomi ke fuskanta ita ce, matsalar hauhawar farashi ta yadda zai zuba jari a harkarsa ta noma har ya ci riba.

Sa’annan, shugaban kungiyar binciken ya yi bayani dangane da yadda wata tsutsa da ake kira da cema ‘Fall Army Worm’, wadda manoman masara a ‘yan shekarun nan muka wayi gari Allah ya jefo mana ita, wanda idan ba a yi sa’a ba sai ka

wayi gari ka ga gonarka da take da yabanya mai kyau, ana sa rai za a samu abin kirki sai ka ga duk daga zuciyarta ta lalace an yi asarar ta baki-daya.

Har ila yau, babban makasudin wannan taro shi ne, tabbatar wa manoma cewa, tana iya yiwuwa a bullo da ingantaccen Iri na masara, wanda zai jure kansa ba tare da an yi masa feshin

magani ba, ma’ana zai iya jure kansa da kansa. Mun gamsu wannan sabon Iri yana da wannan inganci kwarai da gaske, amma mun zo ne domin mu sake jaddada wannan.

Saboda haka, na ke kara jinjina wa manoman da suka yi fice wajen rungumar sababbin fasahohi ba wannan kawai ba, har ma sauran fasahohi na shekarun baya da muka yi ta yi. Idan za ku iya tunawa, wannan cibiya tamu a wannan shekare ne ta cika shekaru dari da daya cif. A wannan zamani na wannan cibiya tamu, mu muka dauki alhakin yada dukkannin wani ingantaccen aikin noma, kama daga rainon ‘ya’yan itatuwa, hatsi, dawa, gero, masara, wake, waken suya da sauran makamantansu har ya zuwa yanzu din nan, kafin a da aka yi garambawul ga irin nauye-nauyen da aka dora mana a sanadiyar sake kirkiro da wasu cibiyoyin binciken aka dan rage mana nauyi.

Akwai wadanda babu abin da ya hada su da noma, amma ganin irin fa’idar da ake samu a cikinsa ya sa suka yi cincirindo suka

rungume shi, saboda haka ina ga mu wadanda muka gaje shi a matsayin sana’a. Babu shakka, noma yana ba wa ‘yan Nijeriya kusan kashi 66 cikin 100, wanda ya yi daidai da kimanin kusan mutum miliyan 160 aikin yi. Saboda haka, duk wani manomi

da ya samu karuwar tattalin arziki, daidai ya ke da kamar ka dauki wani ma’aikaci aiki ka rika biyan sa albashi duk shekara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kungiyoyin CONESAM Sun Baje Kolin Fasahar Sarrafa Kayan Amfanin Gona

Next Post

Bikin Kafuwar Daular Saudiyya Shekara 93: Abubuwan Da Ya Kamata A Sani

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

17 hours ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

18 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

2 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

2 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

3 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

3 weeks ago
Next Post
Bikin Kafuwar Daular Saudiyya Shekara 93: Abubuwan Da Ya Kamata A Sani

Bikin Kafuwar Daular Saudiyya Shekara 93: Abubuwan Da Ya Kamata A Sani

LABARAI MASU NASABA

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Fyade

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

September 6, 2025
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

September 6, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

September 6, 2025
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.