• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cika Shekaru 161: Rundunar Sojojin Nijeriya Ta Tallafawa Marayu 400 A Zamfara

Cika shekaru 161 da kafa Rundunar Sojojin Nijeriya da irin sadaukarwarta a yayin aiki da tunawa da ranar 'yan mazan jiya.

by Muhammad and Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Cika Shekaru 161: Rundunar Sojojin Nijeriya Ta Tallafawa Marayu 400 A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar Sojojin Nijeriya Brigade ta 1 ta gudanar da bikin murnar cika shekaru 161 da kafa rundunar sojojin Nijeriya tare da marayu da yara marasa galihu da kuma dalibai a jihar Zamfara domin tunawa da ranar sojojin a Nijeriya (NADCEL) 2024.

Wannan muhimmiyar rana an sadaukar da ita ne domin karrama jaruman mu da suka mutu ba tare da son ransu ba domin kare al’ummar ‘yan kasa a yayin gudanar da aiki.

  • Dakarun Sojojin Nijeriya Sun Kashe Ƴan Ta’adda 5 Sun KuÉ“utar Da Wasu A Sokoto
  • Garambawul Da Muke Wa Tsarin Aikin Sojojin Nijeriya –Janar Musa

A bikin tunawa da wannan rana, rundunar sojojin Nijeriya Brigade ta 1 da ke Gusau ta gudanar da ayyukan jin kai daban- daban, da suka hada da rabon kayayyakin masarufi, kayan rubutu, tufafi, da rigar kafa ga marayu, marasa galihu, da sauran mabukata a jihar Zamfara.

Birgediya Janar Sani Ahmed, Kwamandan Birgade din ne ya jagoranci rabon kayan sawa ga marayu da mabukata, inda ya jaddada kudirin rundanar sojojin Nijeriya na hada kai da farar hula.

Haka Kuma ya ce wannan shiri dai wani bangare ne na kokarin da Sojoji ke yi na tallafa wa al’ummar farar hula ta hanyoyi daban -daban, da inganta kyakkyawar niyya da karfafa alaka.

Labarai Masu Nasaba

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Janar Ahmed ya bayyana cewa rabon tallafin ya kai kimanin yara marayu da mabukata 400, tare da bayar da littattafan karatun da rubutu da kuma alkalami ga dalibai a fadin makarantun Firamare da Sakandare goma sha daya da ke garin Gusau.

Har ilayau Ya yi nuni da cewa, a yayin da Sojoji ke tallafa wa yankunan karkara, wannan taron ya mayar da hankali ne wajen raba muhimman kayayyaki ga kananan yara, marayu da kuma marasa galihu a garin na Gusau, Inji shi.

Kwamandan Birgade dai yayi amfani da wannan damar wajen yin kira ga al’umma da su hana masu ba da labari ko taimakon ‘yan fashi ta hanyar kai rahoton ayyukansu ga soji. Maimakon haka, ya ja hankalin wadannan ’yan uwa da su tuba su mika makamansu domin dawo da zaman lafiya a jihar da ma sauran jahohin kasar nan, Inji shi.

Kazalika ya bayyana damuwarsa kan ayyukan ‘yan bindiga a jihar, inda ya tabbatar da cewa sojoji suna aiki tukuru don ganin manoma sun yi noma da girbin amfanin gona yadda ya kamata, ta yadda za a tabbatar da samar da abinci da bunkasa tattalin arziki. Ya kuma nemi goyon bayan jama’a da hadin kai ta hanyar baiwa rundunar Sojoji muhimman bayanai domin dawo da zaman lafiya.

Tun da farko, an raba kayayyakin kiwon lafiya ga kananan hukumomi goma sha hudu da ke cikin yankin na Birgediya, an kuma raba littattafan karatun da rubutu na musamman ga daliban firamare, kananan da manyan makarantun sakandare a makarantu goma sha daya da ke Gusau.

Makarantun da suka ci gajiyar wannan karimcin sun hada da Makarantar Firamare ta Nizzamiya, Sabon Garin Gusau, Makarantar Marayu, Karamar firamarai da ke GRA, Gusau, Dan Turai Model Primary School, Hayin Dan Hausa, Sambo sakandare, Tudun Wada, Gusau.

Sauran sun hada da Government Day Secondary School, Unguwan-gwaza Gusau, Government Girls Day Secondary School, Tudun Wada Gusau, General Abdusalam Abubakar Primary School da Kuma wasu gidaje gudu É—ari a cikin garin Gusau, Girls Focal Primary School da Ungwan Zabarma Gusau da Sarkin Kudu Secondary Government Secondary da Government Girls Arabic Secondary School Gusau da NAOWA Creche Nursery and Primary School da kuma Alasawa Gusau.

Wadanda suka ci gajiyar tallafin sun bayyana jin dadin su ga rundunar sojin Nijeriya bisa irin wannan tallafi da aka ba su tare da gudanar da addu’o’i da sakon fatan alheri ga rundanar sojojin ta Nijeriya da kuma gwamnatin jihar Zamfara kan bayar da tallafin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MarayuRundunar sojin NijeriyaTallafiZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Dokar Bai Wa Auren Jinsi Kariya: Gwamnatin Tarayya Ta Koka Kan Rahoton Wata Jarida

Next Post

Mijina Ba Ya Hira Da Ni

Related

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da É—umi-É—uminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

6 hours ago
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu
Labarai

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

7 hours ago
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu
Labarai

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

8 hours ago
Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina
Labarai

Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

9 hours ago
Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa
Manyan Labarai

Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa

12 hours ago
Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32
Manyan Labarai

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

13 hours ago
Next Post
aure

Mijina Ba Ya Hira Da Ni

LABARAI MASU NASABA

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

August 5, 2025
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

August 5, 2025
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

August 5, 2025
Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

August 5, 2025
Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

August 5, 2025
Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

August 5, 2025
Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.