• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cika Shekaru 161: Rundunar Sojojin Nijeriya Ta Tallafawa Marayu 400 A Zamfara

Cika shekaru 161 da kafa Rundunar Sojojin Nijeriya da irin sadaukarwarta a yayin aiki da tunawa da ranar 'yan mazan jiya.

by Muhammad and Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Cika Shekaru 161: Rundunar Sojojin Nijeriya Ta Tallafawa Marayu 400 A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar Sojojin Nijeriya Brigade ta 1 ta gudanar da bikin murnar cika shekaru 161 da kafa rundunar sojojin Nijeriya tare da marayu da yara marasa galihu da kuma dalibai a jihar Zamfara domin tunawa da ranar sojojin a Nijeriya (NADCEL) 2024.

Wannan muhimmiyar rana an sadaukar da ita ne domin karrama jaruman mu da suka mutu ba tare da son ransu ba domin kare al’ummar ‘yan kasa a yayin gudanar da aiki.

  • Dakarun Sojojin Nijeriya Sun Kashe Ƴan Ta’adda 5 Sun Kuɓutar Da Wasu A Sokoto
  • Garambawul Da Muke Wa Tsarin Aikin Sojojin Nijeriya –Janar Musa

A bikin tunawa da wannan rana, rundunar sojojin Nijeriya Brigade ta 1 da ke Gusau ta gudanar da ayyukan jin kai daban- daban, da suka hada da rabon kayayyakin masarufi, kayan rubutu, tufafi, da rigar kafa ga marayu, marasa galihu, da sauran mabukata a jihar Zamfara.

Birgediya Janar Sani Ahmed, Kwamandan Birgade din ne ya jagoranci rabon kayan sawa ga marayu da mabukata, inda ya jaddada kudirin rundanar sojojin Nijeriya na hada kai da farar hula.

Haka Kuma ya ce wannan shiri dai wani bangare ne na kokarin da Sojoji ke yi na tallafa wa al’ummar farar hula ta hanyoyi daban -daban, da inganta kyakkyawar niyya da karfafa alaka.

Labarai Masu Nasaba

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Janar Ahmed ya bayyana cewa rabon tallafin ya kai kimanin yara marayu da mabukata 400, tare da bayar da littattafan karatun da rubutu da kuma alkalami ga dalibai a fadin makarantun Firamare da Sakandare goma sha daya da ke garin Gusau.

Har ilayau Ya yi nuni da cewa, a yayin da Sojoji ke tallafa wa yankunan karkara, wannan taron ya mayar da hankali ne wajen raba muhimman kayayyaki ga kananan yara, marayu da kuma marasa galihu a garin na Gusau, Inji shi.

Kwamandan Birgade dai yayi amfani da wannan damar wajen yin kira ga al’umma da su hana masu ba da labari ko taimakon ‘yan fashi ta hanyar kai rahoton ayyukansu ga soji. Maimakon haka, ya ja hankalin wadannan ’yan uwa da su tuba su mika makamansu domin dawo da zaman lafiya a jihar da ma sauran jahohin kasar nan, Inji shi.

Kazalika ya bayyana damuwarsa kan ayyukan ‘yan bindiga a jihar, inda ya tabbatar da cewa sojoji suna aiki tukuru don ganin manoma sun yi noma da girbin amfanin gona yadda ya kamata, ta yadda za a tabbatar da samar da abinci da bunkasa tattalin arziki. Ya kuma nemi goyon bayan jama’a da hadin kai ta hanyar baiwa rundunar Sojoji muhimman bayanai domin dawo da zaman lafiya.

Tun da farko, an raba kayayyakin kiwon lafiya ga kananan hukumomi goma sha hudu da ke cikin yankin na Birgediya, an kuma raba littattafan karatun da rubutu na musamman ga daliban firamare, kananan da manyan makarantun sakandare a makarantu goma sha daya da ke Gusau.

Makarantun da suka ci gajiyar wannan karimcin sun hada da Makarantar Firamare ta Nizzamiya, Sabon Garin Gusau, Makarantar Marayu, Karamar firamarai da ke GRA, Gusau, Dan Turai Model Primary School, Hayin Dan Hausa, Sambo sakandare, Tudun Wada, Gusau.

Sauran sun hada da Government Day Secondary School, Unguwan-gwaza Gusau, Government Girls Day Secondary School, Tudun Wada Gusau, General Abdusalam Abubakar Primary School da Kuma wasu gidaje gudu ɗari a cikin garin Gusau, Girls Focal Primary School da Ungwan Zabarma Gusau da Sarkin Kudu Secondary Government Secondary da Government Girls Arabic Secondary School Gusau da NAOWA Creche Nursery and Primary School da kuma Alasawa Gusau.

Wadanda suka ci gajiyar tallafin sun bayyana jin dadin su ga rundunar sojin Nijeriya bisa irin wannan tallafi da aka ba su tare da gudanar da addu’o’i da sakon fatan alheri ga rundanar sojojin ta Nijeriya da kuma gwamnatin jihar Zamfara kan bayar da tallafin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MarayuRundunar sojin NijeriyaTallafiZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Dokar Bai Wa Auren Jinsi Kariya: Gwamnatin Tarayya Ta Koka Kan Rahoton Wata Jarida

Next Post

Mijina Ba Ya Hira Da Ni

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

1 hour ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

14 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

15 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

17 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

20 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

22 hours ago
Next Post
aure

Mijina Ba Ya Hira Da Ni

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.