ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cika Shekaru 161: Rundunar Sojojin Nijeriya Ta Tallafawa Marayu 400 A Zamfara

Cika shekaru 161 da kafa Rundunar Sojojin Nijeriya da irin sadaukarwarta a yayin aiki da tunawa da ranar 'yan mazan jiya.

by Muhammad and Umar Faruk
2 years ago
Sojojin Nijeriya

Rundunar Sojojin Nijeriya Brigade ta 1 ta gudanar da bikin murnar cika shekaru 161 da kafa rundunar sojojin Nijeriya tare da marayu da yara marasa galihu da kuma dalibai a jihar Zamfara domin tunawa da ranar sojojin a Nijeriya (NADCEL) 2024.

Wannan muhimmiyar rana an sadaukar da ita ne domin karrama jaruman mu da suka mutu ba tare da son ransu ba domin kare al’ummar ‘yan kasa a yayin gudanar da aiki.

  • Dakarun Sojojin Nijeriya Sun Kashe Ƴan Ta’adda 5 Sun Kuɓutar Da Wasu A Sokoto
  • Garambawul Da Muke Wa Tsarin Aikin Sojojin Nijeriya –Janar Musa

A bikin tunawa da wannan rana, rundunar sojojin Nijeriya Brigade ta 1 da ke Gusau ta gudanar da ayyukan jin kai daban- daban, da suka hada da rabon kayayyakin masarufi, kayan rubutu, tufafi, da rigar kafa ga marayu, marasa galihu, da sauran mabukata a jihar Zamfara.

ADVERTISEMENT

Birgediya Janar Sani Ahmed, Kwamandan Birgade din ne ya jagoranci rabon kayan sawa ga marayu da mabukata, inda ya jaddada kudirin rundanar sojojin Nijeriya na hada kai da farar hula.

Haka Kuma ya ce wannan shiri dai wani bangare ne na kokarin da Sojoji ke yi na tallafa wa al’ummar farar hula ta hanyoyi daban -daban, da inganta kyakkyawar niyya da karfafa alaka.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Janar Ahmed ya bayyana cewa rabon tallafin ya kai kimanin yara marayu da mabukata 400, tare da bayar da littattafan karatun da rubutu da kuma alkalami ga dalibai a fadin makarantun Firamare da Sakandare goma sha daya da ke garin Gusau.

Har ilayau Ya yi nuni da cewa, a yayin da Sojoji ke tallafa wa yankunan karkara, wannan taron ya mayar da hankali ne wajen raba muhimman kayayyaki ga kananan yara, marayu da kuma marasa galihu a garin na Gusau, Inji shi.

Kwamandan Birgade dai yayi amfani da wannan damar wajen yin kira ga al’umma da su hana masu ba da labari ko taimakon ‘yan fashi ta hanyar kai rahoton ayyukansu ga soji. Maimakon haka, ya ja hankalin wadannan ’yan uwa da su tuba su mika makamansu domin dawo da zaman lafiya a jihar da ma sauran jahohin kasar nan, Inji shi.

Kazalika ya bayyana damuwarsa kan ayyukan ‘yan bindiga a jihar, inda ya tabbatar da cewa sojoji suna aiki tukuru don ganin manoma sun yi noma da girbin amfanin gona yadda ya kamata, ta yadda za a tabbatar da samar da abinci da bunkasa tattalin arziki. Ya kuma nemi goyon bayan jama’a da hadin kai ta hanyar baiwa rundunar Sojoji muhimman bayanai domin dawo da zaman lafiya.

Tun da farko, an raba kayayyakin kiwon lafiya ga kananan hukumomi goma sha hudu da ke cikin yankin na Birgediya, an kuma raba littattafan karatun da rubutu na musamman ga daliban firamare, kananan da manyan makarantun sakandare a makarantu goma sha daya da ke Gusau.

Makarantun da suka ci gajiyar wannan karimcin sun hada da Makarantar Firamare ta Nizzamiya, Sabon Garin Gusau, Makarantar Marayu, Karamar firamarai da ke GRA, Gusau, Dan Turai Model Primary School, Hayin Dan Hausa, Sambo sakandare, Tudun Wada, Gusau.

Sauran sun hada da Government Day Secondary School, Unguwan-gwaza Gusau, Government Girls Day Secondary School, Tudun Wada Gusau, General Abdusalam Abubakar Primary School da Kuma wasu gidaje gudu ɗari a cikin garin Gusau, Girls Focal Primary School da Ungwan Zabarma Gusau da Sarkin Kudu Secondary Government Secondary da Government Girls Arabic Secondary School Gusau da NAOWA Creche Nursery and Primary School da kuma Alasawa Gusau.

Wadanda suka ci gajiyar tallafin sun bayyana jin dadin su ga rundunar sojin Nijeriya bisa irin wannan tallafi da aka ba su tare da gudanar da addu’o’i da sakon fatan alheri ga rundanar sojojin ta Nijeriya da kuma gwamnatin jihar Zamfara kan bayar da tallafin.

Sojojin Nijeriya
Muhammad
+ posts Bio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
Sojojin Nijeriya
Umar Faruk
+ posts Bio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnatin Kebbi Ta Amince Da ₦2.07bn Alawus-alawus Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Ibrahim Augie A Zaɓen 2027
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Matashi Ya Shiga Hannu Kan Zargin Wulaƙanta Alƙur’ani A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Miƙa Yara 5 Da Aka Ceto Daga Hannun Masu Safarar Mutane Ga Iyayensu

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Sojojin Nijeriya
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Next Post
aure

Mijina Ba Ya Hira Da Ni

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Sojojin Nijeriya

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Sojojin Nijeriya

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.