ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cika Shekaru 161: Rundunar Sojojin Nijeriya Ta Tallafawa Marayu 400 A Zamfara

Cika shekaru 161 da kafa Rundunar Sojojin Nijeriya da irin sadaukarwarta a yayin aiki da tunawa da ranar 'yan mazan jiya.

by Muhammad and Umar Faruk
2 years ago
Sojojin Nijeriya

Rundunar Sojojin Nijeriya Brigade ta 1 ta gudanar da bikin murnar cika shekaru 161 da kafa rundunar sojojin Nijeriya tare da marayu da yara marasa galihu da kuma dalibai a jihar Zamfara domin tunawa da ranar sojojin a Nijeriya (NADCEL) 2024.

Wannan muhimmiyar rana an sadaukar da ita ne domin karrama jaruman mu da suka mutu ba tare da son ransu ba domin kare al’ummar ‘yan kasa a yayin gudanar da aiki.

  • Dakarun Sojojin Nijeriya Sun Kashe Ƴan Ta’adda 5 Sun Kuɓutar Da Wasu A Sokoto
  • Garambawul Da Muke Wa Tsarin Aikin Sojojin Nijeriya –Janar Musa

A bikin tunawa da wannan rana, rundunar sojojin Nijeriya Brigade ta 1 da ke Gusau ta gudanar da ayyukan jin kai daban- daban, da suka hada da rabon kayayyakin masarufi, kayan rubutu, tufafi, da rigar kafa ga marayu, marasa galihu, da sauran mabukata a jihar Zamfara.

ADVERTISEMENT

Birgediya Janar Sani Ahmed, Kwamandan Birgade din ne ya jagoranci rabon kayan sawa ga marayu da mabukata, inda ya jaddada kudirin rundanar sojojin Nijeriya na hada kai da farar hula.

Haka Kuma ya ce wannan shiri dai wani bangare ne na kokarin da Sojoji ke yi na tallafa wa al’ummar farar hula ta hanyoyi daban -daban, da inganta kyakkyawar niyya da karfafa alaka.

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Janar Ahmed ya bayyana cewa rabon tallafin ya kai kimanin yara marayu da mabukata 400, tare da bayar da littattafan karatun da rubutu da kuma alkalami ga dalibai a fadin makarantun Firamare da Sakandare goma sha daya da ke garin Gusau.

Har ilayau Ya yi nuni da cewa, a yayin da Sojoji ke tallafa wa yankunan karkara, wannan taron ya mayar da hankali ne wajen raba muhimman kayayyaki ga kananan yara, marayu da kuma marasa galihu a garin na Gusau, Inji shi.

Kwamandan Birgade dai yayi amfani da wannan damar wajen yin kira ga al’umma da su hana masu ba da labari ko taimakon ‘yan fashi ta hanyar kai rahoton ayyukansu ga soji. Maimakon haka, ya ja hankalin wadannan ’yan uwa da su tuba su mika makamansu domin dawo da zaman lafiya a jihar da ma sauran jahohin kasar nan, Inji shi.

Kazalika ya bayyana damuwarsa kan ayyukan ‘yan bindiga a jihar, inda ya tabbatar da cewa sojoji suna aiki tukuru don ganin manoma sun yi noma da girbin amfanin gona yadda ya kamata, ta yadda za a tabbatar da samar da abinci da bunkasa tattalin arziki. Ya kuma nemi goyon bayan jama’a da hadin kai ta hanyar baiwa rundunar Sojoji muhimman bayanai domin dawo da zaman lafiya.

Tun da farko, an raba kayayyakin kiwon lafiya ga kananan hukumomi goma sha hudu da ke cikin yankin na Birgediya, an kuma raba littattafan karatun da rubutu na musamman ga daliban firamare, kananan da manyan makarantun sakandare a makarantu goma sha daya da ke Gusau.

Makarantun da suka ci gajiyar wannan karimcin sun hada da Makarantar Firamare ta Nizzamiya, Sabon Garin Gusau, Makarantar Marayu, Karamar firamarai da ke GRA, Gusau, Dan Turai Model Primary School, Hayin Dan Hausa, Sambo sakandare, Tudun Wada, Gusau.

Sauran sun hada da Government Day Secondary School, Unguwan-gwaza Gusau, Government Girls Day Secondary School, Tudun Wada Gusau, General Abdusalam Abubakar Primary School da Kuma wasu gidaje gudu ɗari a cikin garin Gusau, Girls Focal Primary School da Ungwan Zabarma Gusau da Sarkin Kudu Secondary Government Secondary da Government Girls Arabic Secondary School Gusau da NAOWA Creche Nursery and Primary School da kuma Alasawa Gusau.

Wadanda suka ci gajiyar tallafin sun bayyana jin dadin su ga rundunar sojin Nijeriya bisa irin wannan tallafi da aka ba su tare da gudanar da addu’o’i da sakon fatan alheri ga rundanar sojojin ta Nijeriya da kuma gwamnatin jihar Zamfara kan bayar da tallafin.

Sojojin Nijeriya
Muhammad
+ posts Bio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje
Sojojin Nijeriya
Umar Faruk
+ posts Bio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Next Post
aure

Mijina Ba Ya Hira Da Ni

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.