• English
  • Business News
Saturday, May 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cikin Shekara 3 Mun Yi Aiki Tukuru Don Ci Gaban Jihar Gombe —Inuwa Yahaya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Cikin Shekara 3 Mun Yi Aiki Tukuru Don Ci Gaban Jihar Gombe —Inuwa Yahaya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na jihar Gombe, ya ce, sun gabatar da sabbin dabaru, da manufofi da tsare-tsare da nufin kyautata rayuwar al’umar jihar a cikin shekaru ukun da suka gabata, yana mai cewa, sun dage don sadaukar da kai wajen cika alkawurran yakin neman zaben da suka yi.

Gwamna Inuwa Yahaya ya yaba da daurarriyar demokradiyya da aka samu tsawon shekaru 23 ba tare da katsewa ba a Nijeriya, lamarin da ya bayyana cewa shi ne irin sa mafi tsawo a tarihin mulkin farar fula tun bayan samun ‘yancin kai.

  • ‘Kwankwaso Zai Lashe Zaben Shugaban Kasa Na 2023’ —Jideogu Ogbu
  • Lalacewar Babbar Hanyar Lantarki Ta Kasa Na Tabbatar Da Gazawar Nijeriya A Komai – Atiku

Inuwa ya bayyana hakan ne a yayin kaddamar da sabuwar makarantar firamare da karamar sakandare ta Alabura a Anguwar Ƙumbiya-Ƙumbiya da ke fadar jihar, yake cewa, “A bayyane yake cewa demokradiyyar Nijeriya ta kafu, duk da dimbin kalubalen da kasar ke fuskanta. Muna iya fahimta da sasanta kan mu ba tare da daukar makamai ba”.

“Hakan yana kara nuna bunkasar mu a siyasance da tsayin dakan mu duk da bambancin mu na yanki da kabila da addini. Ko shakka babu dawowa mulkin dimokuradiyya a 1999 ya kawo kusanci ga al’umma ta yadda za a magance bukatu da buri na kungiyoyi daban-daban a kasar nan”.

Ya ce a Jihar Gombe, babu shakka cewa dimokuradiyya ta kawowa jihar ci gaba mai dorewa, “Ya zuwa yanzu gwamnatocin farar hula uku suka yi mulki inda mu daga bisani muka biyo baya har yanzu muke cika shekaru uku, mun yi bakin kokarinmu wajen ganin mun kara tabbatar da nasarorin da gwamnatocin da suka gabata suka samu tare da gyara kura-kuran da muka tarar.

Labarai Masu Nasaba

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

“Rahoton bibiyar al’amaura na shekaru ukun da suka gabata ya nuna cewa mun samu kaso 90 cikin dari na nasarori wajen cika alkawuran da muka yiwa al’ummar jihar nan, hakika babban aiki ne wannan, tun da muka iya cika alkawuran da muka yi wa al’ummarmu a wannan lokaci na tabarbarewar tattalin arzikin duniya da rashin tabbas, amma idan muka yi la’akari da jajircewar mu, da aiki tukuru da juriya, da kuma kokarin sarrafa ‘yan kudaden da muke dasu, mun samu damar aiwatar da ayyuka da suka rataya a wuyan mu, wadda hatta abokan adawar siyasar mu sun mika wuya”.

Gwamnan ya ce yayin da gwamnatinsa ke cika shekaru uku a kan karagar mulki, zai ci gaba da maida hankali tare da himmatuwa wajen inganta rayuwar al’umma ta hanyar samar da ababen more rayuwa na kyautata zamantakewar al’umma cikin adalci, da tabbatar da zaman lafiya da tsaro, da doka da oda tare da samar da damammaki ga al’ummar jihar.

Ya bayyana tabbacin cewa ta hanyar samar da tsarin dimokuradiyya ne kawai jihar za ta iya ci gaba da biyan bukatun jama’a tare da tabbatar da amincewar su ga gwamnatin jihar karkashin jagorancin sa. Gwamna Inuwa Yahaya ya yi amfani da damar wajen yaba wa hangen nesa, da jajircewa da kishin kasa na gundumar Kumbiya Kumbiya da suka sadaukar da gidajensu da muhallinsu don bai wa Gwamnati damar kafa makarantar tare da basu tabbacin gwamnati na ci gaba da nuna goyon baya da taimako a gare su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GombeInuwa Yahayaiyuka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kungiyar Ma’aikatan Majalisar Dokoki Ta Nijeriya (PASAN) Sun Janye Yajin Aikinsu

Next Post

A Karon Farko Shugaban Kasar Amurka Joe Biden Zai Kai Ziyara Saudiyya Da Isra’ila

Related

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF
Labarai

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

3 hours ago
Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 
Labarai

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

9 hours ago
NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal
Labarai

NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal

9 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari

10 hours ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

13 hours ago
Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari
Labarai

Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari

16 hours ago
Next Post
A Karon Farko Shugaban Kasar Amurka Joe Biden Zai Kai Ziyara Saudiyya Da Isra’ila

A Karon Farko Shugaban Kasar Amurka Joe Biden Zai Kai Ziyara Saudiyya Da Isra'ila

LABARAI MASU NASABA

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

May 24, 2025
Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

May 24, 2025
Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

May 24, 2025
CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

May 24, 2025

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 24, 2025
Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

May 24, 2025
An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

May 24, 2025
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

May 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.