• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cikin Shekara 3 Mun Yi Aiki Tukuru Don Ci Gaban Jihar Gombe —Inuwa Yahaya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Cikin

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na jihar Gombe, ya ce, sun gabatar da sabbin dabaru, da manufofi da tsare-tsare da nufin kyautata rayuwar al’umar jihar a cikin shekaru ukun da suka gabata, yana mai cewa, sun dage don sadaukar da kai wajen cika alkawurran yakin neman zaben da suka yi.

Gwamna Inuwa Yahaya ya yaba da daurarriyar demokradiyya da aka samu tsawon shekaru 23 ba tare da katsewa ba a Nijeriya, lamarin da ya bayyana cewa shi ne irin sa mafi tsawo a tarihin mulkin farar fula tun bayan samun ‘yancin kai.

  • ‘Kwankwaso Zai Lashe Zaben Shugaban Kasa Na 2023’ —Jideogu Ogbu
  • Lalacewar Babbar Hanyar Lantarki Ta Kasa Na Tabbatar Da Gazawar Nijeriya A Komai – Atiku

Inuwa ya bayyana hakan ne a yayin kaddamar da sabuwar makarantar firamare da karamar sakandare ta Alabura a Anguwar Ƙumbiya-Ƙumbiya da ke fadar jihar, yake cewa, “A bayyane yake cewa demokradiyyar Nijeriya ta kafu, duk da dimbin kalubalen da kasar ke fuskanta. Muna iya fahimta da sasanta kan mu ba tare da daukar makamai ba”.

“Hakan yana kara nuna bunkasar mu a siyasance da tsayin dakan mu duk da bambancin mu na yanki da kabila da addini. Ko shakka babu dawowa mulkin dimokuradiyya a 1999 ya kawo kusanci ga al’umma ta yadda za a magance bukatu da buri na kungiyoyi daban-daban a kasar nan”.

Ya ce a Jihar Gombe, babu shakka cewa dimokuradiyya ta kawowa jihar ci gaba mai dorewa, “Ya zuwa yanzu gwamnatocin farar hula uku suka yi mulki inda mu daga bisani muka biyo baya har yanzu muke cika shekaru uku, mun yi bakin kokarinmu wajen ganin mun kara tabbatar da nasarorin da gwamnatocin da suka gabata suka samu tare da gyara kura-kuran da muka tarar.

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

“Rahoton bibiyar al’amaura na shekaru ukun da suka gabata ya nuna cewa mun samu kaso 90 cikin dari na nasarori wajen cika alkawuran da muka yiwa al’ummar jihar nan, hakika babban aiki ne wannan, tun da muka iya cika alkawuran da muka yi wa al’ummarmu a wannan lokaci na tabarbarewar tattalin arzikin duniya da rashin tabbas, amma idan muka yi la’akari da jajircewar mu, da aiki tukuru da juriya, da kuma kokarin sarrafa ‘yan kudaden da muke dasu, mun samu damar aiwatar da ayyuka da suka rataya a wuyan mu, wadda hatta abokan adawar siyasar mu sun mika wuya”.

Gwamnan ya ce yayin da gwamnatinsa ke cika shekaru uku a kan karagar mulki, zai ci gaba da maida hankali tare da himmatuwa wajen inganta rayuwar al’umma ta hanyar samar da ababen more rayuwa na kyautata zamantakewar al’umma cikin adalci, da tabbatar da zaman lafiya da tsaro, da doka da oda tare da samar da damammaki ga al’ummar jihar.

Ya bayyana tabbacin cewa ta hanyar samar da tsarin dimokuradiyya ne kawai jihar za ta iya ci gaba da biyan bukatun jama’a tare da tabbatar da amincewar su ga gwamnatin jihar karkashin jagorancin sa. Gwamna Inuwa Yahaya ya yi amfani da damar wajen yaba wa hangen nesa, da jajircewa da kishin kasa na gundumar Kumbiya Kumbiya da suka sadaukar da gidajensu da muhallinsu don bai wa Gwamnati damar kafa makarantar tare da basu tabbacin gwamnati na ci gaba da nuna goyon baya da taimako a gare su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Next Post
A Karon Farko Shugaban Kasar Amurka Joe Biden Zai Kai Ziyara Saudiyya Da Isra’ila

A Karon Farko Shugaban Kasar Amurka Joe Biden Zai Kai Ziyara Saudiyya Da Isra'ila

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.