• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cikin Shekara 3 Mun Yi Aiki Tukuru Don Ci Gaban Jihar Gombe —Inuwa Yahaya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Cikin Shekara 3 Mun Yi Aiki Tukuru Don Ci Gaban Jihar Gombe —Inuwa Yahaya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na jihar Gombe, ya ce, sun gabatar da sabbin dabaru, da manufofi da tsare-tsare da nufin kyautata rayuwar al’umar jihar a cikin shekaru ukun da suka gabata, yana mai cewa, sun dage don sadaukar da kai wajen cika alkawurran yakin neman zaben da suka yi.

Gwamna Inuwa Yahaya ya yaba da daurarriyar demokradiyya da aka samu tsawon shekaru 23 ba tare da katsewa ba a Nijeriya, lamarin da ya bayyana cewa shi ne irin sa mafi tsawo a tarihin mulkin farar fula tun bayan samun ‘yancin kai.

  • ‘Kwankwaso Zai Lashe Zaben Shugaban Kasa Na 2023’ —Jideogu Ogbu
  • Lalacewar Babbar Hanyar Lantarki Ta Kasa Na Tabbatar Da Gazawar Nijeriya A Komai – Atiku

Inuwa ya bayyana hakan ne a yayin kaddamar da sabuwar makarantar firamare da karamar sakandare ta Alabura a Anguwar Ƙumbiya-Ƙumbiya da ke fadar jihar, yake cewa, “A bayyane yake cewa demokradiyyar Nijeriya ta kafu, duk da dimbin kalubalen da kasar ke fuskanta. Muna iya fahimta da sasanta kan mu ba tare da daukar makamai ba”.

“Hakan yana kara nuna bunkasar mu a siyasance da tsayin dakan mu duk da bambancin mu na yanki da kabila da addini. Ko shakka babu dawowa mulkin dimokuradiyya a 1999 ya kawo kusanci ga al’umma ta yadda za a magance bukatu da buri na kungiyoyi daban-daban a kasar nan”.

Ya ce a Jihar Gombe, babu shakka cewa dimokuradiyya ta kawowa jihar ci gaba mai dorewa, “Ya zuwa yanzu gwamnatocin farar hula uku suka yi mulki inda mu daga bisani muka biyo baya har yanzu muke cika shekaru uku, mun yi bakin kokarinmu wajen ganin mun kara tabbatar da nasarorin da gwamnatocin da suka gabata suka samu tare da gyara kura-kuran da muka tarar.

Labarai Masu Nasaba

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

“Rahoton bibiyar al’amaura na shekaru ukun da suka gabata ya nuna cewa mun samu kaso 90 cikin dari na nasarori wajen cika alkawuran da muka yiwa al’ummar jihar nan, hakika babban aiki ne wannan, tun da muka iya cika alkawuran da muka yi wa al’ummarmu a wannan lokaci na tabarbarewar tattalin arzikin duniya da rashin tabbas, amma idan muka yi la’akari da jajircewar mu, da aiki tukuru da juriya, da kuma kokarin sarrafa ‘yan kudaden da muke dasu, mun samu damar aiwatar da ayyuka da suka rataya a wuyan mu, wadda hatta abokan adawar siyasar mu sun mika wuya”.

Gwamnan ya ce yayin da gwamnatinsa ke cika shekaru uku a kan karagar mulki, zai ci gaba da maida hankali tare da himmatuwa wajen inganta rayuwar al’umma ta hanyar samar da ababen more rayuwa na kyautata zamantakewar al’umma cikin adalci, da tabbatar da zaman lafiya da tsaro, da doka da oda tare da samar da damammaki ga al’ummar jihar.

Ya bayyana tabbacin cewa ta hanyar samar da tsarin dimokuradiyya ne kawai jihar za ta iya ci gaba da biyan bukatun jama’a tare da tabbatar da amincewar su ga gwamnatin jihar karkashin jagorancin sa. Gwamna Inuwa Yahaya ya yi amfani da damar wajen yaba wa hangen nesa, da jajircewa da kishin kasa na gundumar Kumbiya Kumbiya da suka sadaukar da gidajensu da muhallinsu don bai wa Gwamnati damar kafa makarantar tare da basu tabbacin gwamnati na ci gaba da nuna goyon baya da taimako a gare su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GombeInuwa Yahayaiyuka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kungiyar Ma’aikatan Majalisar Dokoki Ta Nijeriya (PASAN) Sun Janye Yajin Aikinsu

Next Post

A Karon Farko Shugaban Kasar Amurka Joe Biden Zai Kai Ziyara Saudiyya Da Isra’ila

Related

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Labarai

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

1 hour ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

2 hours ago
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
Labarai

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

3 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

4 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

5 hours ago
Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
Labarai

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

6 hours ago
Next Post
A Karon Farko Shugaban Kasar Amurka Joe Biden Zai Kai Ziyara Saudiyya Da Isra’ila

A Karon Farko Shugaban Kasar Amurka Joe Biden Zai Kai Ziyara Saudiyya Da Isra'ila

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.