ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cikin Shekara 3 Mun Yi Aiki Tukuru Don Ci Gaban Jihar Gombe —Inuwa Yahaya

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Cikin

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na jihar Gombe, ya ce, sun gabatar da sabbin dabaru, da manufofi da tsare-tsare da nufin kyautata rayuwar al’umar jihar a cikin shekaru ukun da suka gabata, yana mai cewa, sun dage don sadaukar da kai wajen cika alkawurran yakin neman zaben da suka yi.

Gwamna Inuwa Yahaya ya yaba da daurarriyar demokradiyya da aka samu tsawon shekaru 23 ba tare da katsewa ba a Nijeriya, lamarin da ya bayyana cewa shi ne irin sa mafi tsawo a tarihin mulkin farar fula tun bayan samun ‘yancin kai.

  • ‘Kwankwaso Zai Lashe Zaben Shugaban Kasa Na 2023’ —Jideogu Ogbu
  • Lalacewar Babbar Hanyar Lantarki Ta Kasa Na Tabbatar Da Gazawar Nijeriya A Komai – Atiku

Inuwa ya bayyana hakan ne a yayin kaddamar da sabuwar makarantar firamare da karamar sakandare ta Alabura a Anguwar Ƙumbiya-Ƙumbiya da ke fadar jihar, yake cewa, “A bayyane yake cewa demokradiyyar Nijeriya ta kafu, duk da dimbin kalubalen da kasar ke fuskanta. Muna iya fahimta da sasanta kan mu ba tare da daukar makamai ba”.

ADVERTISEMENT

“Hakan yana kara nuna bunkasar mu a siyasance da tsayin dakan mu duk da bambancin mu na yanki da kabila da addini. Ko shakka babu dawowa mulkin dimokuradiyya a 1999 ya kawo kusanci ga al’umma ta yadda za a magance bukatu da buri na kungiyoyi daban-daban a kasar nan”.

Ya ce a Jihar Gombe, babu shakka cewa dimokuradiyya ta kawowa jihar ci gaba mai dorewa, “Ya zuwa yanzu gwamnatocin farar hula uku suka yi mulki inda mu daga bisani muka biyo baya har yanzu muke cika shekaru uku, mun yi bakin kokarinmu wajen ganin mun kara tabbatar da nasarorin da gwamnatocin da suka gabata suka samu tare da gyara kura-kuran da muka tarar.

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

“Rahoton bibiyar al’amaura na shekaru ukun da suka gabata ya nuna cewa mun samu kaso 90 cikin dari na nasarori wajen cika alkawuran da muka yiwa al’ummar jihar nan, hakika babban aiki ne wannan, tun da muka iya cika alkawuran da muka yi wa al’ummarmu a wannan lokaci na tabarbarewar tattalin arzikin duniya da rashin tabbas, amma idan muka yi la’akari da jajircewar mu, da aiki tukuru da juriya, da kuma kokarin sarrafa ‘yan kudaden da muke dasu, mun samu damar aiwatar da ayyuka da suka rataya a wuyan mu, wadda hatta abokan adawar siyasar mu sun mika wuya”.

Gwamnan ya ce yayin da gwamnatinsa ke cika shekaru uku a kan karagar mulki, zai ci gaba da maida hankali tare da himmatuwa wajen inganta rayuwar al’umma ta hanyar samar da ababen more rayuwa na kyautata zamantakewar al’umma cikin adalci, da tabbatar da zaman lafiya da tsaro, da doka da oda tare da samar da damammaki ga al’ummar jihar.

Ya bayyana tabbacin cewa ta hanyar samar da tsarin dimokuradiyya ne kawai jihar za ta iya ci gaba da biyan bukatun jama’a tare da tabbatar da amincewar su ga gwamnatin jihar karkashin jagorancin sa. Gwamna Inuwa Yahaya ya yi amfani da damar wajen yaba wa hangen nesa, da jajircewa da kishin kasa na gundumar Kumbiya Kumbiya da suka sadaukar da gidajensu da muhallinsu don bai wa Gwamnati damar kafa makarantar tare da basu tabbacin gwamnati na ci gaba da nuna goyon baya da taimako a gare su.

Cikin
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Next Post
A Karon Farko Shugaban Kasar Amurka Joe Biden Zai Kai Ziyara Saudiyya Da Isra’ila

A Karon Farko Shugaban Kasar Amurka Joe Biden Zai Kai Ziyara Saudiyya Da Isra'ila

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.