• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CNSA: Kasar Sin Na Kiyaye Ra’ayin Bude Kofa Da Kasar Amurka Wajen Yin Mu’amalan Ayyukan Sararin Samaniya

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
CNSA: Kasar Sin Na Kiyaye Ra’ayin Bude Kofa Da Kasar Amurka Wajen Yin Mu’amalan Ayyukan Sararin Samaniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan baya, wasu rahotanni na nuna cewa, wai jakadan kasar Amurka dake kasar Sin R. Nicholas Burns ya ce, kasar Sin ba ta da shirin yin haɗin gwiwa da Amurka a fannin binciken duniyar wata. Dangane da wannan batu, kakakin hukumar kula da harkokin binciken sararin samaniya ta kasar Sin wato CNSA Xu Hongliang ya bayyana wa kafofin watsa labarai cewa, kasar Sin tana tsayawa tsayin daka wajen aiwatar da ayyukan sararin samaniya da yin amfani da albarkatun sararin samaniya cikin lumana. Kuma tana fatan yin shawarwari da hadin gwiwa da kasashen duniya bisa tushen adalci da cimma moriyar juna, yin amfani da albarkatun sararin samaniya cikin lumana, da nuna fahimtar juna da neman ci gaba, ta yadda za a ba da kwarin gwiwar karfafa dunkulewar bil Adama ta fuskar nazarin harkokin sararin samaniya.

Kasar Sin tana mai da hankali matuka a fannin hadin gwiwar binciken harkokin sararin samaniya, kuma tana kiyaye ra’ayin bude kofa wajen yin shawarwari da kasar Amurka kan ayyukan da abin ya shafa. Kana, kasar Sin tana maraba da masanan kasar Amurka da ma sauran kasashen duniya, da su neman izni ta hanyoyin da suka dace, bisa bayanin da kasar Sin ta fidda, a duk lokacin da suke son gudanar da nazari kan samfurorin da ’yan sama jannatin kasar Sin suka dawo da su duniyarmu daga duniyar wata.

  • Sin Za Ta Daidaita Haraji Kan Hajojin Da Ake Shige Da Ficen Su A 2024
  • Sin Ta Kara Tallafin Kudi Don Maido Da Wuraren Kiyaye Ruwa A Yankunan Da Girgizar Kasar Ta Shafa

Kasar Sin ba ta taba fidda wata takarda ko manufar kin hadin gwiwa da kasar Amurka ba. Amma, akwai masana da dama na kasashen duniya da suka taba yin kira ga kasar Amurka da ta kawar da dokar “Wolf Act”, wadda ta hana yin hadin gwiwa da kasar Sin kan ayyukan nazarin sararin samaniya.

Kakakin ya kara da cewa, kasar Sin na fatan kwararrun kasar Amurka za su taimaka wajen soke wannan doka, ta yadda za a gudanar da nazari kan sararin samaniya cikin hadin gwiwa, da ba da karin tallafi ga al’ummar kasashen duniya. Hakika kasar Sin tana fatan habaka hadin gwiwar dake tsakaninta da kasashen duniya wajen aiwatar da ayyukan nazarin samarin samaniya.

Sannan mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin ma ya ce, har kullum Sin na maraba da Amurka a fannin musaya da hadin gwiwar ayyukan da suka shafi binciken sararin samaniya. Wang ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai na Juma’ar nan.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Wasu rahotannin baya bayan nan sun hakaito jakadan Amurka a kasar Sin Robert Nicholas Burns, na cewa wai Sin ba ta da niyyar yin hadin gwiwa da Amurka a fannin binciken duniyar wata, kuma fannin zai kasance wani fage guda ga kasashen biyu.

Game da hakan, Wang Wenbin ya ce gwamnatin kasar Sin ta sha bayyana aniyarta ta bunkasa bincike, da amfani da sararin samaniya ta hanyoyin zaman lafiya, kuma a shirye take ta gudanar da musaya, da hadin gwiwa tare da sauran kasashen duniya bisa daidaito, da cimma moriya tare, da kuma bunkasa fannin tare da juna, da ingiza gina al’umma mai makomar bai daya a fannin binciken sararin samaniya.

Wang Wenbin ya jaddada cewa, idan har da gaske ne Amurka na son ingiza musaya, da hadin gwiwa tare da Sin a wannan fanni, to kamata ya yi ta kawar da dokokin ta dake yin tarnaki ga hakan, ta kuma dakatar da bayyana kalamai marasa dacewa, kana ta aiwatar da matakai na zahiri, na kawar da duk wani shinge dake dakile hadin gwiwar sassan biyu. (Masu Fassarawa: Maryam Yang, Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rahoto: Sin Ta Kasance A Kan Gaba A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani A Asiya

Next Post

Mun Yi Watsi Da Akidun Shirin AGILE – Gwamnatin Kaduna

Related

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

7 hours ago
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

8 hours ago
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

9 hours ago
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
Daga Birnin Sin

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

10 hours ago
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

11 hours ago
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
Daga Birnin Sin

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

12 hours ago
Next Post
2023: Kotu Ta Tabbatar Da Uba Sani A Matsayin Dan Takarar Gwamnan APC A Kaduna

Mun Yi Watsi Da Akidun Shirin AGILE - Gwamnatin Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.