ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CNSA: Kasar Sin Na Kiyaye Ra’ayin Bude Kofa Da Kasar Amurka Wajen Yin Mu’amalan Ayyukan Sararin Samaniya

by CGTN Hausa
3 years ago
CNSA

Kwanan baya, wasu rahotanni na nuna cewa, wai jakadan kasar Amurka dake kasar Sin R. Nicholas Burns ya ce, kasar Sin ba ta da shirin yin haɗin gwiwa da Amurka a fannin binciken duniyar wata. Dangane da wannan batu, kakakin hukumar kula da harkokin binciken sararin samaniya ta kasar Sin wato CNSA Xu Hongliang ya bayyana wa kafofin watsa labarai cewa, kasar Sin tana tsayawa tsayin daka wajen aiwatar da ayyukan sararin samaniya da yin amfani da albarkatun sararin samaniya cikin lumana. Kuma tana fatan yin shawarwari da hadin gwiwa da kasashen duniya bisa tushen adalci da cimma moriyar juna, yin amfani da albarkatun sararin samaniya cikin lumana, da nuna fahimtar juna da neman ci gaba, ta yadda za a ba da kwarin gwiwar karfafa dunkulewar bil Adama ta fuskar nazarin harkokin sararin samaniya.

Kasar Sin tana mai da hankali matuka a fannin hadin gwiwar binciken harkokin sararin samaniya, kuma tana kiyaye ra’ayin bude kofa wajen yin shawarwari da kasar Amurka kan ayyukan da abin ya shafa. Kana, kasar Sin tana maraba da masanan kasar Amurka da ma sauran kasashen duniya, da su neman izni ta hanyoyin da suka dace, bisa bayanin da kasar Sin ta fidda, a duk lokacin da suke son gudanar da nazari kan samfurorin da ’yan sama jannatin kasar Sin suka dawo da su duniyarmu daga duniyar wata.

  • Sin Za Ta Daidaita Haraji Kan Hajojin Da Ake Shige Da Ficen Su A 2024
  • Sin Ta Kara Tallafin Kudi Don Maido Da Wuraren Kiyaye Ruwa A Yankunan Da Girgizar Kasar Ta Shafa

Kasar Sin ba ta taba fidda wata takarda ko manufar kin hadin gwiwa da kasar Amurka ba. Amma, akwai masana da dama na kasashen duniya da suka taba yin kira ga kasar Amurka da ta kawar da dokar “Wolf Act”, wadda ta hana yin hadin gwiwa da kasar Sin kan ayyukan nazarin sararin samaniya.

ADVERTISEMENT

Kakakin ya kara da cewa, kasar Sin na fatan kwararrun kasar Amurka za su taimaka wajen soke wannan doka, ta yadda za a gudanar da nazari kan sararin samaniya cikin hadin gwiwa, da ba da karin tallafi ga al’ummar kasashen duniya. Hakika kasar Sin tana fatan habaka hadin gwiwar dake tsakaninta da kasashen duniya wajen aiwatar da ayyukan nazarin samarin samaniya.

Sannan mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin ma ya ce, har kullum Sin na maraba da Amurka a fannin musaya da hadin gwiwar ayyukan da suka shafi binciken sararin samaniya. Wang ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai na Juma’ar nan.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Wasu rahotannin baya bayan nan sun hakaito jakadan Amurka a kasar Sin Robert Nicholas Burns, na cewa wai Sin ba ta da niyyar yin hadin gwiwa da Amurka a fannin binciken duniyar wata, kuma fannin zai kasance wani fage guda ga kasashen biyu.

Game da hakan, Wang Wenbin ya ce gwamnatin kasar Sin ta sha bayyana aniyarta ta bunkasa bincike, da amfani da sararin samaniya ta hanyoyin zaman lafiya, kuma a shirye take ta gudanar da musaya, da hadin gwiwa tare da sauran kasashen duniya bisa daidaito, da cimma moriya tare, da kuma bunkasa fannin tare da juna, da ingiza gina al’umma mai makomar bai daya a fannin binciken sararin samaniya.

Wang Wenbin ya jaddada cewa, idan har da gaske ne Amurka na son ingiza musaya, da hadin gwiwa tare da Sin a wannan fanni, to kamata ya yi ta kawar da dokokin ta dake yin tarnaki ga hakan, ta kuma dakatar da bayyana kalamai marasa dacewa, kana ta aiwatar da matakai na zahiri, na kawar da duk wani shinge dake dakile hadin gwiwar sassan biyu. (Masu Fassarawa: Maryam Yang, Saminu Alhassan)

CNSA
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

MASU ALAKA

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Daga Birnin Sin

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin
Daga Birnin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Next Post
2023: Kotu Ta Tabbatar Da Uba Sani A Matsayin Dan Takarar Gwamnan APC A Kaduna

Mun Yi Watsi Da Akidun Shirin AGILE - Gwamnatin Kaduna

LABARAI MASU NASABA

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.