• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Ɗumi-Ɗumi: Jam’iyyar APC Ta Kori Shugabanta Na Jihar Bauchi, Aliyu Misau

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Da Ɗumi-Ɗumi: Jam’iyyar APC Ta Kori Shugabanta Na Jihar Bauchi, Aliyu Misau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabannin jam’iyyar APC a jihar Bauchi sun cimma matsayar korar shugaban jam’iyyar na jihar Bauchi, Alhaji Babayo Aliyu Misau biyo bayan yanke tsammani ga salon jagorancinsa.

Bayan da suka sallami shugaban, sun kuma amince da naɗa mataimakinsa, Alhaji Muhammad Hassan Tilde a matsayin shugaban riƙon ƙwarya.

  • Tsohon Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Henry Kissinger, Ya Mutu Yana Da Shekaru 100
  • Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Kwamitin Mutum 8 Don Inganta Harkokin Aikin Hajjin 2024

Shugabannin jam’iyyar waɗanda suka cimma wannan matsayar a zaman da suka gudanar a ranar Alhamis, inda suka ce, gaza iya shugabanci na Aliyu Misau ta sanya har jama’an jihar sun fara yanke ƙauna daga jam’iyyar don haka dole su ɗauki matakin kiyaye martabar jam’iyyar.

Da ya ke karanta wa ‘yan jarida matsayar shugabannin, mai bai wa jam’iyyar APC shawara kan harkokin Shari’a a jihar Bauchi, Barista Rabiu Garba, ya ce, bisa rashin iya shugabancin Babayo Aliyu Misau, jam’iyyar tana rasa tasirinta.

Ya ce, tun rikice-rikicen da aka samu a lokacin zaɓen cikin gida na jam’iyyar sun samu asali ne daga rashin iya shugabancin Misau, don haka suka yanke tsammani daga gareshi tare da cire shi baki ɗaya.

Labarai Masu Nasaba

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

Barista Garba ta ce, “Biyo bayan zaman da shugabannin jam’iyyar APC a matakin jihar Bauchi suka yi, kamar yadda kuke gani, a cikin shugabanni 37, muna da mutum 27 da muka cimma matsaya guda, mun cimma matsaya, kowa ya amince tare da sanya hannu kan takara inda muka sauƙe tare da yanke tsammani daga shugabancin Alhaji Babayo Aliyu Misau a matsayin shugaban jam’iyyar APC a jihar Bauchi.

“Dalili kuwa, saboda gazawa da ya yi na yin jagorancin jam’iyya kamar yadda kundin tsarin mulkin jam’iyya ya tsara. Kuma mun gaya masa a lokuta daban-daban ya gyara, ya ɗauki alƙawarin zai gyara amma har zuwa yanzu bai gyara ba.

“Kuma mun zo muka ga an kai wani matakin da ‘yan jihar Bauchi da shugabanninmu da zaɓaɓɓu da manyan shugabanninmu sun yanke tsammani daga shugabancinsa, kusan babu wanda yake goyon bayansa saboda an san ba zai kaimu ga gaci ba.

“Don haka muka ga dole mu yi wa kanmu ƙiyamullaili muka kira wannan zaman a yau domin amincewa da sauƙe shi.

“Mun yi amfani da sashi 17 (5) na kundin tsarin mulkin jam’iyyar APC ta 2022 (da aka yi wa kwaskwarima) muka sauƙe Alh. Babayo Aliyu Misau a matsayin shugaba.

“Sannan ƙarƙashin sashi 17 (6) na kundin tsarin jam’iyyar muka naɗa mataimakinsa Alh. Mohammed Hassan Tilde a matsayin shugaban jam’iyyar APC na jihar Bauchi na riƙon kwarya.

“Kamar yadda kundin tsarin mulkin jam’iyyar ta tsara, za mu rubuta wannan abun a rubuce za mu kai wa uwar jam’iyyar APC a Abuja za mu kai wa shugaban APC na ƙasa mu shaida masa abun da muka cimma.”

Kazalika, ya ce, bisa rashin iya jagorancin na Misau, jam’iyyar ta rasa kujeru da yawa a zaɓen 2023, kuma dole su ɗauki matakan da suka dace na farfaɗo da martabar jam’iyyar.

Kan shari’unsu da suke kotuna kuwa, Rabiu ya nuna cewa wannan sallamar na Misau ba zai shafi harƙoƙin Shari’a da jam’iyyar take yi ba, ya nuna kwarin guiwar cewa za su samu nasarori a shari’unsu da ke ake kan yi.

Da ya ke jawabin amsar mulki, shugaban riƙon ƙwarya na jam’iyyar, Alhaji Muhammad Hassan Tilde, ya yi alƙawarin gudanar da shugabanci na kwarai tare da haɗa kan mambobin jam’iyyar a dukkanin matakai.

Ya nemi goyon bayan mambobi da shugabannin jam’iyyar domin ci gaban jam’iyyar da jihar Bauchi baki ɗaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCBauchiKauran Bauchi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Kashi 91.4 Sun Yaba Da Gudummawar Sin Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Next Post

Zargin Rufe Masallatai Mataki Ne Na Haifar Da Rudani

Related

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

1 hour ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

2 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

2 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

3 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

5 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

6 hours ago
Next Post
Zargin Rufe Masallatai Mataki Ne Na Haifar Da Rudani

Zargin Rufe Masallatai Mataki Ne Na Haifar Da Rudani

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.