• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Ɗumi-Ɗumi: Jam’iyyar APC Ta Kori Shugabanta Na Jihar Bauchi, Aliyu Misau

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Da Ɗumi-Ɗumi: Jam’iyyar APC Ta Kori Shugabanta Na Jihar Bauchi, Aliyu Misau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabannin jam’iyyar APC a jihar Bauchi sun cimma matsayar korar shugaban jam’iyyar na jihar Bauchi, Alhaji Babayo Aliyu Misau biyo bayan yanke tsammani ga salon jagorancinsa.

Bayan da suka sallami shugaban, sun kuma amince da naɗa mataimakinsa, Alhaji Muhammad Hassan Tilde a matsayin shugaban riƙon ƙwarya.

  • Tsohon Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Henry Kissinger, Ya Mutu Yana Da Shekaru 100
  • Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Kwamitin Mutum 8 Don Inganta Harkokin Aikin Hajjin 2024

Shugabannin jam’iyyar waɗanda suka cimma wannan matsayar a zaman da suka gudanar a ranar Alhamis, inda suka ce, gaza iya shugabanci na Aliyu Misau ta sanya har jama’an jihar sun fara yanke ƙauna daga jam’iyyar don haka dole su ɗauki matakin kiyaye martabar jam’iyyar.

Da ya ke karanta wa ‘yan jarida matsayar shugabannin, mai bai wa jam’iyyar APC shawara kan harkokin Shari’a a jihar Bauchi, Barista Rabiu Garba, ya ce, bisa rashin iya shugabancin Babayo Aliyu Misau, jam’iyyar tana rasa tasirinta.

Ya ce, tun rikice-rikicen da aka samu a lokacin zaɓen cikin gida na jam’iyyar sun samu asali ne daga rashin iya shugabancin Misau, don haka suka yanke tsammani daga gareshi tare da cire shi baki ɗaya.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

Barista Garba ta ce, “Biyo bayan zaman da shugabannin jam’iyyar APC a matakin jihar Bauchi suka yi, kamar yadda kuke gani, a cikin shugabanni 37, muna da mutum 27 da muka cimma matsaya guda, mun cimma matsaya, kowa ya amince tare da sanya hannu kan takara inda muka sauƙe tare da yanke tsammani daga shugabancin Alhaji Babayo Aliyu Misau a matsayin shugaban jam’iyyar APC a jihar Bauchi.

“Dalili kuwa, saboda gazawa da ya yi na yin jagorancin jam’iyya kamar yadda kundin tsarin mulkin jam’iyya ya tsara. Kuma mun gaya masa a lokuta daban-daban ya gyara, ya ɗauki alƙawarin zai gyara amma har zuwa yanzu bai gyara ba.

“Kuma mun zo muka ga an kai wani matakin da ‘yan jihar Bauchi da shugabanninmu da zaɓaɓɓu da manyan shugabanninmu sun yanke tsammani daga shugabancinsa, kusan babu wanda yake goyon bayansa saboda an san ba zai kaimu ga gaci ba.

“Don haka muka ga dole mu yi wa kanmu ƙiyamullaili muka kira wannan zaman a yau domin amincewa da sauƙe shi.

“Mun yi amfani da sashi 17 (5) na kundin tsarin mulkin jam’iyyar APC ta 2022 (da aka yi wa kwaskwarima) muka sauƙe Alh. Babayo Aliyu Misau a matsayin shugaba.

“Sannan ƙarƙashin sashi 17 (6) na kundin tsarin jam’iyyar muka naɗa mataimakinsa Alh. Mohammed Hassan Tilde a matsayin shugaban jam’iyyar APC na jihar Bauchi na riƙon kwarya.

“Kamar yadda kundin tsarin mulkin jam’iyyar ta tsara, za mu rubuta wannan abun a rubuce za mu kai wa uwar jam’iyyar APC a Abuja za mu kai wa shugaban APC na ƙasa mu shaida masa abun da muka cimma.”

Kazalika, ya ce, bisa rashin iya jagorancin na Misau, jam’iyyar ta rasa kujeru da yawa a zaɓen 2023, kuma dole su ɗauki matakan da suka dace na farfaɗo da martabar jam’iyyar.

Kan shari’unsu da suke kotuna kuwa, Rabiu ya nuna cewa wannan sallamar na Misau ba zai shafi harƙoƙin Shari’a da jam’iyyar take yi ba, ya nuna kwarin guiwar cewa za su samu nasarori a shari’unsu da ke ake kan yi.

Da ya ke jawabin amsar mulki, shugaban riƙon ƙwarya na jam’iyyar, Alhaji Muhammad Hassan Tilde, ya yi alƙawarin gudanar da shugabanci na kwarai tare da haɗa kan mambobin jam’iyyar a dukkanin matakai.

Ya nemi goyon bayan mambobi da shugabannin jam’iyyar domin ci gaban jam’iyyar da jihar Bauchi baki ɗaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCBauchiKauran Bauchi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Kashi 91.4 Sun Yaba Da Gudummawar Sin Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Next Post

Zargin Rufe Masallatai Mataki Ne Na Haifar Da Rudani

Related

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

1 hour ago
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

3 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

4 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

7 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

7 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

8 hours ago
Next Post
Zargin Rufe Masallatai Mataki Ne Na Haifar Da Rudani

Zargin Rufe Masallatai Mataki Ne Na Haifar Da Rudani

LABARAI MASU NASABA

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.