ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Rufe Masallatai Mataki Ne Na Haifar Da Rudani

by CGTN Hausa
3 years ago
Masallatai

Tun da jimawa, mun sha ji, da ganin rahotanni dake zargin cewa wai mahukunta a kasar Sin na rushe masallatai, ko mayar da su wuraren aikata wasu harkoki na daban. Irin wadannan rahotanni da wasu kafofin watsa labaran yammacin duniya ke yadawa na da matukar hadari, kasancewar suna kunshe da zarge-zarge marasa tushe, da karairayi marasa shaidu na zahiri.

A baya bayan nan, wata kafar watsa labarai ta yammacin duniya ta rawaito zargin da hukumar kare hakkin dan’adam ta “Human Right Watch” ko HRW ta yi, cewa wai ana samun karuwar ruguza tsarin addinai a shekarun baya-bayan nan a kasar Sin, kuma wai Sin na kara azamar neman karfin iko kan addinai.

  • Gwamnan Bauchi Ya Gabatar Da Biliyan 300 A Matsayin Kasafin Kudin 2024
  • Kwace Wa NNPP Zaben Kano Na Iya Haddasa Tashin Hankali A Afrika – NNPP

Cikin wannan zargi akwai abubuwan lura da yawa, amma kadan daga cikinsu akwai batun rashin shaidu na hakika, ko korafi daga musulmin kasar dake zaune a wuraren da aka yi zargin. Wato dai idan har HRW na da gaskiya kan zargin da ta yi, kamata ya yi ta bayyana shaidun gani da ido, ba wai cewa wai “An gano daga hotunan tauraron dan Adam” ba!

ADVERTISEMENT

Kaza lika da yake rahoton na HRW ya ce mahukuntan Sin na kokarin samun karin iko kan addinai, ba wai addinin musulunci kadai ba, abun tambayar shi ne wane irin iko ne Sin za ta samu idan ta dakile addinai da mabiyansu?

Ga duk mai son sanin ainihin gaskiyar halin da musulmi, da mabiya sauran addinai suke ciki a kasar Sin, hanya daya mafi sauki ita ce ya bibiyi rahotanni daga mazauna kasar, ko dai Sinawa ’yan kasa, ko baki mazauna kasar dake neman ilimi, ko gudanar da harkokin kasuwanci da sauransu, wadanda za su fadi gaskiyar lamari bisa abubuwan da suka gani da idanun su, ba wai jita-jita daga kafofin dake adawa da ci gaban kasar Sin ba.

LABARAI MASU NASABA

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Ko shakka babu kasar Sin na da tsare-tsare daban daban na kare kima, da martabar addinai, da hakkokin mabiya addinai bisa doka. Alal misali, a ranar 3 ga watan Afirilun shekarar 2018, ofishin watsa labarai na majalissar gudanarwar kasar Sin, ya fitar da takardar bayanai mai taken Manufofi da ayyukan Sin na kare ’yancin bin addinai”, wadda a ciki aka zayyana matakan da kasar ke bi na tabbatar da kowa ya yi addinin da ya zaba bisa radin kansa, da tabbatar da zaman jituwa tsakanin mabiya addinai daban daban, da ma wadanda ba sa bin kowane addini.

Kaza lika, takardar ta yi bayani filla-filla, game da matakan da Sin ke bi na tabbatar da an martaba ikon mabiya addinai na yin ibada ba tare da tsangwama ba, da inganta wuraren ibada, ta yadda mabiya addinai da wadanda ba sa bin kowane addini za su rayu cikin jituwa.

A nan birnin Beijing ga misali, akwai gwamman masallatai dake sassan gundumomin birnin daban daban, wadanda musulmi ke amfani da su a ko da yaushe don gudanar da ibada, kuma tsawon sama da shekaru 10 da nake halartar masallatan dake cikin birnin, ban taba ji ko ganin an rushe wani masallaci ba! Hakan ya tabbatar min da cewa akwai wasu boyayyu, kuma munanan manufofi, a zukatan masu kitsawa, da yada jita-jitar rushe masallatai a Sin.

Daga karshe akwai bukatar mu rika taka-tsantan da kafofin dake yada labaran karya domin cimma burin siyasa. Domin ko ba komai, sauraro da aiki da irin wadannan labarai na bogi, na iya haifar da rashin jituwa, da tada hankulan al’umma, da haifar da tashe-tashen hankula, musamman a irin wannan lokaci da duniya ta fi bukatar hadin kai, da zaman lafiya sama da kowane lokaci a tarihi.

Masallatai
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

MASU ALAKA

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
Daga Birnin Sin

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Next Post
Bikin CISCE Ya Jawo Hankalin Kamfanonin Amurka Da Kasashen Turai

Bikin CISCE Ya Jawo Hankalin Kamfanonin Amurka Da Kasashen Turai

LABARAI MASU NASABA

Morocco Na Fargabar Rashin Ƴan Wasa 2 Gabanin Karawa Da Brazil

Morocco Na Fargabar Rashin Ƴan Wasa 2 Gabanin Karawa Da Brazil

June 8, 2026
Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

June 8, 2026
Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

June 8, 2026
Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.