• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Abokin Daka Ake Shan Gari

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A matsayina na dan kasar waje dake kaunar al’adun kasashen Afirka, har kullum ina fatan ganin an samu ci gaban tattalin arziki a kasashen Afirka, inda hadin kan kasashen Afirka da kasar Sin ya kan karfafa min gwiwar samun biyan wannan bukata.

A jiya Laraba ne, aka gudanar da wani taron karfafa zuba jari a kasar Nijar, a birnin Changsha dake tsakiyar kasar Sin. Inda wani kamfanin kasar Sin ya sa hannu kan yarjejeniyar kafa wani yankin masana’antu na musamman a kasar ta Nijar, don taimakawa kasar a kokarinta na raya bangaren masana’antu mai alaka da sarrafa amfanin gona da ma’adinai. An gudanar da wannan taro ne karkashin laimar bikin baje kolin harkokin tattalin arziki da ciniki na kasar Sin da kasashen Afirka na CAETE, wanda aka kaddamar a yau Alhamis, duk a birnin na Changsha dake kasar Sin.

  • Kungiyar Musulmi Ta Kasar Sin Ta Gudanar Da Liyafar Bikin Babbar Sallah

A kan gudanar da bikin baje koli na CAETE a Changsha bayan ko wadanne shekaru biyu-biyu, wanda ya kasance wani muhimmin dandali, inda gwamnatoci da kamfanonin kasashen Afirka da na Sin suke mu’amala don neman kulla alakar hadin gwiwa. Bikin na bana dai ya shafi ayyuka masu alaka da gina kayayyakin more rayuwa da ba sa gurbata muhalli, da kiwon lafiya, da sarrafa amfanin gona, da gina yankunan masana’antu, da horar da matasa da ilimin sana’o’i, da sauransu. Ya zuwa yanzu wasu kamfanoni 1500 daga kasashe 29 sun tabbatar da niyyarsu ta nuna kayayyakinsu.

Haka kuma ana shirin kulla kwangiloli 218 a yayin bikin, wadanda darajarsu za ta kai dalar Amurka biliyan 19.1. Ban da haka, kasar Najeriya na daga cikin kasashen Afirka 8 da aka gayyata a matsayin muhimman baki a bikin na wannan karo, inda za ta nuna wasu kayayyakin da ake samarwa a kasar, a wani wuri na musamman da aka kebe mata cikin dakin baje kolin kayayyaki.

Shaidu da dama sun tabbatar da yadda hadin gwiwar Afirka da Sin ke amfanar kasashen Afirka. Misali, albarkacin yadda kasar Sin ta soke harajin da ake karba kan wasu kayayyakin da ake shigo da su cikin kasuwannin kasar Sin daga wasu kasashen dake nahiyar Afirka, da sauran manufofin da Sin ta gabatar, dimbin kayayyakin kasashen Afirka, misali ganyen shayi na ti na kasar Kenya, da ridi na kasar Habasha, da dai sauransu, sun fara shiga kasuwannin kasar Sin, lamarin da ya taimaka wa manoman wadannan kasashe samun karin kudin shiga.

Labarai Masu Nasaba

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Bayanai na nuna cewa, ko da a kasuwar Gaoqiao dake lardin Hunan na kasar Sin kadai, an shigar da waken gahawa da darajarsa ta kai dalar Amukra miliyan 10, cikin kasar Sin, daga kasashen Afirka, a shekarar 2022. Kana ana sa ran ganin wannan adadi ya ninka a bana.

Ban da wannan kuma, wani shafin yanar gizo na sayar da kayayyaki mai taken Kilimall, da wani kamfanin kasar Sin ya kafa, yana samun karbuwa a nahiyar Afirka. Yanzu kamfanoni da daidaikun mutane fiye da 8000 na kasashen Afirka da na kasar Sin sun bude kantuna fiye da 12000 a kan wannan shafin yanar gizo, inda ake sayar da wasu nau’ikan kayayyaki kimanin miliyan 1. Kana an ce a kasar Kenya kadai, wannan shafin yanar gizo ya taimaka wajen samar da karin guraben aikin yi fiye da 5000.

Haka zalika, za a iya ganin karin nasarorin da aka cimma ta fuskar hadin gwiwar kasashen Afirka da kasar Sin a bangaren gina kayayyakin more rayuwa. Inda a kasar Najeriya, tashar jiragen ruwa ta Lekki da wani kamfanin kasar Sin ya gina za ta taimakawa birnin Legas wajen zama cibiyar jigilar kayayyaki ta jiragen ruwa mafi girma a tsakiya da yammacin Afirka, kana za ta samar da sabbin guraben aikin yi kimanin dubu 200 cikin shekaru masu zuwa. A kasar Aljeriya kuma, wata tashar samar da wutar lantarki bisa zafin rana, tana samar da wutar lantarki a kai a kai ga wasu kauyukan da suke cikin hamadar Sahara. Sa’an nan a kasar Ghana, na’urorin zamani na sadarwa da aka sanya a yankunan karkarar kasar na samar da hidima ga manoman kasar fiye da miliyan 3.

Tambaya a nan ita ce, me ya sa hadin gwiwar dake tsakanin bangarorin Afirka da Sin ke sanya kasashen Afirka ci gaba? Amsar ita ce, shugabannin kasar Sin sun riga sun tabbatar da manufar kasar game da hadin gwiwa da kasashen Afirka, tun kusan shekaru 10 da suka wuce, wato: Kokarin zama aminiyar kasashen Afirka, da nuna musu sahihanci, da taimaka musu samun hakikanin ci gaba, gami da mai da adalci a gaban moriya yayin da take hadin gwiwa da kasashen Afirka.

Kamar yadda babban jigon bikin CAETE na wannan karo ya nuna, wato “neman samun ci gaba tare, da more wata kyakkyawar makoma a nan gaba tare”, ya nuna cewa, kasar Sin a ko da yaushe tana neman hadin gwiwa tare da kasashen Afirka don su ci gaba tare. Masu iya magana na cewa da abokin daka ake shan gari, yayin da yake tafiya kan turbar neman ci gaban kasa, kuma ba zai nemi a shawo kanka, ko kuma hana ci gabanka ta hanyar daukar wasu matakai na kashin kai ba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gini Mai Hawa Biyu Ya Rufta A Garin Fatakwal

Next Post

Yadda Tallafin Gaggawa Da Kasar Sin Ta Samarwa Zimbabwe Ya Kara Fito Da Manufar Kawancen Gargajiya Tsakanin Sassan Biyu

Related

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

2 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

4 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

4 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

21 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

21 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

23 hours ago
Next Post
Yadda Tallafin Gaggawa Da Kasar Sin Ta Samarwa Zimbabwe Ya Kara Fito Da Manufar Kawancen Gargajiya Tsakanin Sassan Biyu

Yadda Tallafin Gaggawa Da Kasar Sin Ta Samarwa Zimbabwe Ya Kara Fito Da Manufar Kawancen Gargajiya Tsakanin Sassan Biyu

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.