• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Abokin Daka Ake Shan Gari

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A matsayina na dan kasar waje dake kaunar al’adun kasashen Afirka, har kullum ina fatan ganin an samu ci gaban tattalin arziki a kasashen Afirka, inda hadin kan kasashen Afirka da kasar Sin ya kan karfafa min gwiwar samun biyan wannan bukata.

A jiya Laraba ne, aka gudanar da wani taron karfafa zuba jari a kasar Nijar, a birnin Changsha dake tsakiyar kasar Sin. Inda wani kamfanin kasar Sin ya sa hannu kan yarjejeniyar kafa wani yankin masana’antu na musamman a kasar ta Nijar, don taimakawa kasar a kokarinta na raya bangaren masana’antu mai alaka da sarrafa amfanin gona da ma’adinai. An gudanar da wannan taro ne karkashin laimar bikin baje kolin harkokin tattalin arziki da ciniki na kasar Sin da kasashen Afirka na CAETE, wanda aka kaddamar a yau Alhamis, duk a birnin na Changsha dake kasar Sin.

  • Kungiyar Musulmi Ta Kasar Sin Ta Gudanar Da Liyafar Bikin Babbar Sallah

A kan gudanar da bikin baje koli na CAETE a Changsha bayan ko wadanne shekaru biyu-biyu, wanda ya kasance wani muhimmin dandali, inda gwamnatoci da kamfanonin kasashen Afirka da na Sin suke mu’amala don neman kulla alakar hadin gwiwa. Bikin na bana dai ya shafi ayyuka masu alaka da gina kayayyakin more rayuwa da ba sa gurbata muhalli, da kiwon lafiya, da sarrafa amfanin gona, da gina yankunan masana’antu, da horar da matasa da ilimin sana’o’i, da sauransu. Ya zuwa yanzu wasu kamfanoni 1500 daga kasashe 29 sun tabbatar da niyyarsu ta nuna kayayyakinsu.

Haka kuma ana shirin kulla kwangiloli 218 a yayin bikin, wadanda darajarsu za ta kai dalar Amurka biliyan 19.1. Ban da haka, kasar Najeriya na daga cikin kasashen Afirka 8 da aka gayyata a matsayin muhimman baki a bikin na wannan karo, inda za ta nuna wasu kayayyakin da ake samarwa a kasar, a wani wuri na musamman da aka kebe mata cikin dakin baje kolin kayayyaki.

Shaidu da dama sun tabbatar da yadda hadin gwiwar Afirka da Sin ke amfanar kasashen Afirka. Misali, albarkacin yadda kasar Sin ta soke harajin da ake karba kan wasu kayayyakin da ake shigo da su cikin kasuwannin kasar Sin daga wasu kasashen dake nahiyar Afirka, da sauran manufofin da Sin ta gabatar, dimbin kayayyakin kasashen Afirka, misali ganyen shayi na ti na kasar Kenya, da ridi na kasar Habasha, da dai sauransu, sun fara shiga kasuwannin kasar Sin, lamarin da ya taimaka wa manoman wadannan kasashe samun karin kudin shiga.

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

Kayan Aro Baya Rufe Katara

Bayanai na nuna cewa, ko da a kasuwar Gaoqiao dake lardin Hunan na kasar Sin kadai, an shigar da waken gahawa da darajarsa ta kai dalar Amukra miliyan 10, cikin kasar Sin, daga kasashen Afirka, a shekarar 2022. Kana ana sa ran ganin wannan adadi ya ninka a bana.

Ban da wannan kuma, wani shafin yanar gizo na sayar da kayayyaki mai taken Kilimall, da wani kamfanin kasar Sin ya kafa, yana samun karbuwa a nahiyar Afirka. Yanzu kamfanoni da daidaikun mutane fiye da 8000 na kasashen Afirka da na kasar Sin sun bude kantuna fiye da 12000 a kan wannan shafin yanar gizo, inda ake sayar da wasu nau’ikan kayayyaki kimanin miliyan 1. Kana an ce a kasar Kenya kadai, wannan shafin yanar gizo ya taimaka wajen samar da karin guraben aikin yi fiye da 5000.

Haka zalika, za a iya ganin karin nasarorin da aka cimma ta fuskar hadin gwiwar kasashen Afirka da kasar Sin a bangaren gina kayayyakin more rayuwa. Inda a kasar Najeriya, tashar jiragen ruwa ta Lekki da wani kamfanin kasar Sin ya gina za ta taimakawa birnin Legas wajen zama cibiyar jigilar kayayyaki ta jiragen ruwa mafi girma a tsakiya da yammacin Afirka, kana za ta samar da sabbin guraben aikin yi kimanin dubu 200 cikin shekaru masu zuwa. A kasar Aljeriya kuma, wata tashar samar da wutar lantarki bisa zafin rana, tana samar da wutar lantarki a kai a kai ga wasu kauyukan da suke cikin hamadar Sahara. Sa’an nan a kasar Ghana, na’urorin zamani na sadarwa da aka sanya a yankunan karkarar kasar na samar da hidima ga manoman kasar fiye da miliyan 3.

Tambaya a nan ita ce, me ya sa hadin gwiwar dake tsakanin bangarorin Afirka da Sin ke sanya kasashen Afirka ci gaba? Amsar ita ce, shugabannin kasar Sin sun riga sun tabbatar da manufar kasar game da hadin gwiwa da kasashen Afirka, tun kusan shekaru 10 da suka wuce, wato: Kokarin zama aminiyar kasashen Afirka, da nuna musu sahihanci, da taimaka musu samun hakikanin ci gaba, gami da mai da adalci a gaban moriya yayin da take hadin gwiwa da kasashen Afirka.

Kamar yadda babban jigon bikin CAETE na wannan karo ya nuna, wato “neman samun ci gaba tare, da more wata kyakkyawar makoma a nan gaba tare”, ya nuna cewa, kasar Sin a ko da yaushe tana neman hadin gwiwa tare da kasashen Afirka don su ci gaba tare. Masu iya magana na cewa da abokin daka ake shan gari, yayin da yake tafiya kan turbar neman ci gaban kasa, kuma ba zai nemi a shawo kanka, ko kuma hana ci gabanka ta hanyar daukar wasu matakai na kashin kai ba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gini Mai Hawa Biyu Ya Rufta A Garin Fatakwal

Next Post

Yadda Tallafin Gaggawa Da Kasar Sin Ta Samarwa Zimbabwe Ya Kara Fito Da Manufar Kawancen Gargajiya Tsakanin Sassan Biyu

Related

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

3 hours ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Daga Birnin Sin

Kayan Aro Baya Rufe Katara

4 hours ago
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

5 hours ago
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 
Daga Birnin Sin

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

6 hours ago
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

7 hours ago
Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa

8 hours ago
Next Post
Yadda Tallafin Gaggawa Da Kasar Sin Ta Samarwa Zimbabwe Ya Kara Fito Da Manufar Kawancen Gargajiya Tsakanin Sassan Biyu

Yadda Tallafin Gaggawa Da Kasar Sin Ta Samarwa Zimbabwe Ya Kara Fito Da Manufar Kawancen Gargajiya Tsakanin Sassan Biyu

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.