• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-dumi: APC Ta Dakatar Da Dan Majalisar Wakilai Shehu Koko 

byUmar Faruk
2 years ago
Shehu koko

Kwamitin Aiki na jam’iyyar APC (SWC) na jihar Kebbi ya amince da dakatar da dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Koko-Besse/Maiyama a jihar Kebbi, Hon. Shehu Muhammad Koko daga halartar ayyukan jam’iyyar.

 

Dakatarwar ta biyo bayan jerin korafe-korafen da kwamitin ya samu da kuma kaddamar da shi kan dan jam’iyyar daga karamar hukumarsa ta Koko-Besse kan zarge-zargen ayyukan kin jinin jam’iyyar da ya aikata, wanda hakan zai iya bata musu rai ko kuma ya haifar da wata matsala wadda ke iya sa rashin tasiri na jam’iyyar ko zama cikin ƙkiyayya, raini, izgili ko hargitsa tatsuniyoyi da ketar dokoki da ka’idoji, yanke shawara na jam’iyyar.

  • Kayayyaki Marasa Inganci: Hukumar SON Za Ta Yi Wa Dokokinta Kwaskwarima 

Hakan dukka na kunshe ne ta cikin takardar dakatarwar wadda shugaban jam’iyyar na jihar Abubakar Muhammad Kana ya sanya wa hannu kuma aka rabawa manema labarai a Birnin Kebbi a ranar Alhamis.

 

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Takardar dakatarwar ta ci gaba da bayyana cewa, “Shiga ayyukan rashin gaskiya, gudanar da wasu ayyukan na yaki da Jam’iyyar da ke kawo cikas ga tsarin zaman lafiya da bin doka da oda; wadanda ba su dace da manufofin jam’iyyar sabanin sashi na 21 (2) (i) (ii) (vi) (vii) (viii) na kundin tsarin mulkin jam’iyyar APC (2022 da aka yi wa kwaskwarima).”

Shehu koko

Don haka kwamitin ayyuka na jam’iyyar na jihar (SWC) na jam’iyyar na sanar da jama’a cewa, “Kwamitin ayyuka na jihar ya amince da dakatar da Hon. Shehu Muhammad Koko daga shiga duk wata harka ta APC har sai an kammala binciken korafe-korafen.”

 

Bugu da kari, an gargade shi da ya daina bayyana kansa a matsayin dan jam’iyyar APC, kuma kada ya shiga duk wani aiki na jam’iyyar har sai an kammala bincike.

 

A cewar wata majiya mai tushe ta ce Hon. Shehu Muhammad Koko a halin yanzu shi ne shugaban kwamitin rundunar sojojin sama kuma daya daga cikin na hannun daman Kakakin majalisar wakilai kuma mai goyon bayan zababben shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Ko Meye Ya Yi Zafi Mane Ya Nushe Sane Bayan Shan Kaye

Ko Meye Ya Yi Zafi Mane Ya Nushe Sane Bayan Shan Kaye

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version