• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-dumi: APC Ta Dakatar Da Dan Majalisar Wakilai Shehu Koko 

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Da Dumi-dumi: APC Ta Dakatar Da Dan Majalisar Wakilai Shehu Koko 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin Aiki na jam’iyyar APC (SWC) na jihar Kebbi ya amince da dakatar da dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Koko-Besse/Maiyama a jihar Kebbi, Hon. Shehu Muhammad Koko daga halartar ayyukan jam’iyyar.

 

Dakatarwar ta biyo bayan jerin korafe-korafen da kwamitin ya samu da kuma kaddamar da shi kan dan jam’iyyar daga karamar hukumarsa ta Koko-Besse kan zarge-zargen ayyukan kin jinin jam’iyyar da ya aikata, wanda hakan zai iya bata musu rai ko kuma ya haifar da wata matsala wadda ke iya sa rashin tasiri na jam’iyyar ko zama cikin ƙkiyayya, raini, izgili ko hargitsa tatsuniyoyi da ketar dokoki da ka’idoji, yanke shawara na jam’iyyar.

  • Kayayyaki Marasa Inganci: Hukumar SON Za Ta Yi Wa Dokokinta Kwaskwarima 

Hakan dukka na kunshe ne ta cikin takardar dakatarwar wadda shugaban jam’iyyar na jihar Abubakar Muhammad Kana ya sanya wa hannu kuma aka rabawa manema labarai a Birnin Kebbi a ranar Alhamis.

 

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Takardar dakatarwar ta ci gaba da bayyana cewa, “Shiga ayyukan rashin gaskiya, gudanar da wasu ayyukan na yaki da Jam’iyyar da ke kawo cikas ga tsarin zaman lafiya da bin doka da oda; wadanda ba su dace da manufofin jam’iyyar sabanin sashi na 21 (2) (i) (ii) (vi) (vii) (viii) na kundin tsarin mulkin jam’iyyar APC (2022 da aka yi wa kwaskwarima).”

Shehu koko

Don haka kwamitin ayyuka na jam’iyyar na jihar (SWC) na jam’iyyar na sanar da jama’a cewa, “Kwamitin ayyuka na jihar ya amince da dakatar da Hon. Shehu Muhammad Koko daga shiga duk wata harka ta APC har sai an kammala binciken korafe-korafen.”

 

Bugu da kari, an gargade shi da ya daina bayyana kansa a matsayin dan jam’iyyar APC, kuma kada ya shiga duk wani aiki na jam’iyyar har sai an kammala bincike.

 

A cewar wata majiya mai tushe ta ce Hon. Shehu Muhammad Koko a halin yanzu shi ne shugaban kwamitin rundunar sojojin sama kuma daya daga cikin na hannun daman Kakakin majalisar wakilai kuma mai goyon bayan zababben shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Shirya Tsaf Don Sake Yin Zabe A Jihohin Adamawa, Kebbi– INEC

Next Post

Ko Meye Ya Yi Zafi Mane Ya Nushe Sane Bayan Shan Kaye

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

9 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

11 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

12 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

12 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

14 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

16 hours ago
Next Post
Ko Meye Ya Yi Zafi Mane Ya Nushe Sane Bayan Shan Kaye

Ko Meye Ya Yi Zafi Mane Ya Nushe Sane Bayan Shan Kaye

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.