Gwamnatin tarayya ta sauya ranar kidayar yawan jama’a da gidaje na shekarar 2023 da aka tsara yi a ranar 29 ga Maris, 2023.
Ministan yada labarai da al’adu, Lai Mohammed ne ya bayyana hakan ga manema labarai a ranar Laraba jim kadan bayan kammala taron mako-mako na majalisar zartarwa ta tarayya (FEC) wanda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranta a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
A cewar Ministan, a yanzu za a gudanar da kidayar a watan Mayu, 2023.
ADVERTISEMENT
Ya kuma bayyana cewa majalisar ta amince da fitar da kudi naira biliyan 2.8 ga hukumar kidaya ta kasa NPC domin sayo wasu manhajojin komfuta da za a yi amfani da su wajen gudanar da kidayar.














