• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Tasa Ƙeyar Dr. Idris Kan Zargin Kalaman Batanci Ga Manzon Allah

Za Mu Bi Masa Kadinsa, In Ji Almajiran Malamin

by yahuzajere
2 years ago
Manzon Allah

Kotu ta aike da fitaccen malamin addinin a jihar Bauchi, Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi gidan yari bisa zarginsa kalaman tada zaune tsaye da ke barazana ga zaman lafiya.

Malamin wanda ya amsa gayyatar ‘yansanda a ranar Litinin daga bisani suka gurfanar da shi a gaban kotu bisa zargin tada zaune tsaye.

  • Ina Da Yakinin Samun Nasara A Kotu -Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi

Bayanan da ke zuwa mana na cewa ‘yansandan sun gurfanar da shi ne a gaban kotun Majistire ta 1.

Kotun ta tura shi zuwa gidan yarin kafin daga bisani a cigaba da sauraron karar da ‘yansanda suka shigar da shi a gobe Talata.

Da yake tabbatar da kamun da aka yi wa malamin, Shugaban kungiyar, Majalisar Matasa Masu Neman Hadin Kan Malamai Da Cigaban Al’ummar Jihar Bauchi, Yusuf A. Jibrin, ya bayyana cewar malamin ya je wajen ‘yansanda domin amsa gayyatar da suka yi masa ne amma daga bisani suka gurfanar da shi a gaban kotu.

LABARAI MASU NASABA

Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar

NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Ya ce: “Na san da gayyatar da aka yi wa Malam daga hukumar ‘yansanda wanda a yau da safe (Litinin) aka tabbatar mana da cewa Malam ya amsa wannan gayyatar. A da kam ma mun shirya har da ni muka ce za mu je mu yi masa rakiya. Amma da muka yi waya da Allaramma sai ya ce mana a’a malam ya ce bai bukatar kowa ya je. Zai je shi kadai da direba da Malam Ya’u.

“Dazu kuma sai shi Allaramma ya kirani yake ce min an kai Malam gidan Yari. Yake ce min har an kaishi kotu, kotu kuma ta turashi gidan yari.”

Yusuf ya ce, dukkanin abun da ake cajin malamin nasu a kai abu ne da ya shafi akidarsu, “Wannan maganar da malam ya yi akidarmu ne a kai kuma muke fatan Allah ya karbi rayukanmu, kuma manufarmu daya kuma a kanta muke.”

A cewarsa, malaminsu ya koyar da su zaman lafiya da kwanciyar hankali, don haka za su bi dukkanin matakan da suka dace a doron shari’a wajen nema wa malaminsu hakkinsa.

Shugaban, ya bayyana cewar su na ta kokarin kwantar wa almajiran malamin hankali da su kwantar da hankalinsu yayin da ake cigaba da bin matakan da suka dace wajen ganin malamin ya samu ‘yanci.

“Muna kira ga mutanenmu da su kasance cikin zaman lafiya kuma za mu bi lamarin a bisa tsarin doka domin mu tabbatar mun bi kadin abun da aka mana,” Yusuf A. Jibrin ya shaida.

LEADERSHIP HAUSA ta labarto cewa, a kwanakin baya ne Malamin na Ahlul Sunnah Dakta IdrisAbdul’aziz Dutsen Tanshi ya yi furucin cewa ‘…Ko taimakon Manzon Allah ma ba su bukata. Kafin nan ya jero sunayen wasu Shehunnan Darika inda ya nuna cewa ba a neman agajinsu a yayin neman taimako ko a lokacin da ake cikin yanayi na musifa.

Bayan yin jawabin nan nasa ne wasu ke ganin rashin ladabi wajen shigo da Manzon Allah (SAW) cikin misalinsa wanda kai tsaye wasu suka nuna hakan da rashin kimanta Manzon Allah. A kan hakan, hukumar shari’a ta jihar Bauchi ta aike da wasikar gayyata ga Malam Idris domin ya bayyana a gaban malamai domin wanke kansa ko kare kansa sai dai bayan caa da malaman da ke goyan bayansa suka yi hakan ya gagara ba tare da an samu yin wannan mukabalar ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
Manyan Labarai

Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Manyan Labarai

NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa

October 31, 2025
Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi
Manyan Labarai

Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi

October 31, 2025
Next Post
Xi Ya Amsa Wasikar Daliban Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya

Xi Ya Amsa Wasikar Daliban Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

October 31, 2025
Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar

Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa

October 31, 2025

Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda

October 31, 2025
Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi

Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai

October 31, 2025
Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare

Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare

October 31, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

October 31, 2025
Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta

Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.