ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Da Yakinin Samun Nasara A Kotu -Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Dan takarar Gwamnan Jihar Bauchi a zaben 2023 a jam’iyyar APC, Sadique Baba Abubakar, ya nuna kwarin guiwar cewa zai samu nasarar a kotun sauraren kararrakin zabe.

Abubakar ya ce a zaben da aka gudanar shi ne ya samu nasara kuma yana da tulin hujjojin da za su gabatar a gaban kotun sauraron kararrakin zabe da hakan zai kai a dawo masa da wadanda suka zabe shi kujerar.

  • Ranar Ma’aikata: NLC Ta Bukaci Daidaita Albashin Ma’aikata A Kebbi
  • NAFDAC Ta Haramta Shigo Da Indomie Saboda Zargin Sanya Ciwon Daji

A hirarsa da ‘yan jarida bayan dawowarsa daga tafiya a ranar Litinin a Bauchi, Sadique ya ce, sashin shari’a a kasar nan yanzu ya ingantu don haka yana da cikakken kwarin guiwar za su wanzar da adalci da gaskiya a tsakani.

ADVERTISEMENT

“Nasara a hannun Allah ya ke. Mun tabbatar zalumci aka yi kuma da izinin Allah, Allah zai kwato hakkin jama’a. Sannan mun tabbatar yanayin shari’a na Nijeriya na da kyau don mutane ne adilai wadanda za su tabbatar da gaskiya.”

A cewarsa, “Muna godiya wa Allah (SWT) wanda ya ba mu dama muka dawo bayan mun fara wannan gwagwarmayar da muka sanya a gaba na tabbatar da cewa an kwato hakkin jama’a an maida musu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

“Wannan gwagwarmayar mun dauke shi kuma da izinin Allah, Allah zai ba mu nasara a kai.”

Ya gode wa jama’a bisa addu’o’in da ya ce sun yi masa musamman a lokacin azumi da kuma fatan alkairi da suke masa, kana ya kuma jinjina wa kokarin jam’iyyar APC da ta yi kuma take musu. Sai ya nemi masoya da magoya bayansa da su cigaba da kasance masu bin doka da oda har zuwa lokacin da kotu za ya saurari kararsa.

Abubakar ya tabbatar da cewa za su ci gaba da neman hakkinsu babu dare ko rana jar sai sun tabbatar sun kwace mulki, “Ina da kwarin guiwar Allah zai kwato wa jama’a hakkinsu domin Allah ya san abun da ya faru a lokacin zaben nan kuma mun tabbatar matakan da muka dauka za su fito da abubuwan da ake nema na ganin an kwato hakkin jama’a an dawo da shi.

“Na tabbatar da jama’anmu ba su bukatar cigaba da tsarin da ba a biyan albashi, tsarin da yara ke karatu a kasa alhalin ana nan ana gina manya-manyan ofisoshi na biliyoyi wanda ba shi ne ya dami al’umma ba.

“Saboda haka ganin yadda mutane suka ba mu hadin kai a ziyarar da muka kai kananan hukumomi muka ga ya wajaba a kanmu mu cigaba da wannan gwagwarmayar har sai mun tabbatar an kwato hakkin jama’a.”

Idan za ku tuna dai a zaben da aka fafata na 2023 da jam’iyyun siyasa daban-daban guda 14 suka shiga aka fafata da su, sakamakon ya nuna cewa Gwamnan da ke kan kujerar Bala Muhammad na jam’iyyar PDP ya samu nasarar tazarce da kuri’u 525, 280 yayin da abokin hamayyarsa na kusa-kusa Sadique Baba Abubakar ya tashi da kuri’u 432, 272 kamar yadda INEC ta shelanta. To sai dai Abubakar ya kalubanci sakamakon a gaban kotu.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Next Post
Dalibin Islamiyya Ya Gina Gadar Miliyan 12.8 A Ogun

Dalibin Islamiyya Ya Gina Gadar Miliyan 12.8 A Ogun

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.