Kotun sauraren kararrakin zaben gwamnan jihar Nasarawa ta bayar da umarnin janye takardar shaidar cin zabe da aka baiwa gwamna Abdullahi Sule na jam’iyyar APC a zaben gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 18, ga watan Maris, 2023.
Kotun ta kuma bayar da umarnin ba dan takarar jam’iyyar PDP, David Umbugadu, a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan.
Kotun mai alkalai uku ta yanke hukuncin ne ranar litinin, wanda ya tabbatar da Umbugadu a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp