• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-dumi: Shugaban Hukumar ‘Yansanda, Musiliu Smith Ya Yi Murabus

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Musiliu Smith

Shugaban hukumar kula da ‘yansandan Nijeriya (PSC), Musiliu Smith ya yi murabus daga kan mukaminsa.

Wannan matakin dai na zuwa ne bayan rashin jituwa da kai ruwa-rana da aka yi ta samu a tsakanin hukumar da Sufeto Janar na ‘yansandan Nijeriya, Usman Baba Alkali, dangane da batun daukan sabbin ‘yansanda, karin girma wa jami’ai, daukan Kwansitabul da wasu jami’ai.

  • ‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa 3, Sun Ceto Wani Yaro Dan Wata 13 A Edo

Lamarin har ta kai Majalisar koli na hukumar ta bukaci Smith da ya yi murabus cikin ruwan sanyi kuma ya amince da yin haka.

Smith, wanda tsohon Sufeto Janar na ‘yansanda ne, ana sa ran zai mika ragamar mulkin hukumar ga Justice Clara Ogunbiyi (Mai ritaya) wanda shi ne wakilin sashin shari’a a hukumar.

Kakakin hukumar kula da harkokin ‘yansandan Nijeriya, Ikechukwu Ani, ya tabbatar da ajiye aikin Mista Musiliu Smith a ranar Laraba.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

LEADERSHIP Hausa ta nakalto cewa an dauki ‘yan kwanaki ana kai ruwa rana a tsakanin bangarorin biyu wanda a dokance hukumar ce ke da damar gudanar da aikin daukan ‘yansanda.

Ita dai PSC ta wallafa tallar daukan sabbin jami’an ‘yansanda masu mukamin Kwansitabul (constables) tare da bukatar masu sha’awar nema da su cika bukatar hakan a shafinta.

Sai dai kuma daga baya rundunar ‘yansanda ta nemi jama’a da su yi watsi da wannan sanarwar, ta kage kai da fata cewa shirye-shiryen daukan ikonta ne.

Bisa wannan rashin jituwa da fahimtar juna da aka samu, a ranar 24 g watan Agustan, hadakar kungiyar hukumar kula da ‘yansanda suka ayyana tafiya yajin aikin sai baabaa ta gani ga hukumar gudanarwa dangane da abun da suka kira saba yarjejeniya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Next Post
A Bana Jiragen Kasa Na Sin Da Kasashen Turai Sun Yi Tafiye-Tafiye Fiye Da Dubu 10

A Bana Jiragen Kasa Na Sin Da Kasashen Turai Sun Yi Tafiye-Tafiye Fiye Da Dubu 10

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.