• English
  • Business News
Wednesday, May 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Tsohon Sakataren Gwamnatin Enugu Da Wasu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Zamfara, Sun Kashe Mutum Daya, Sun Sace Wasu 8 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da tsohon sakataren gwamnatin Jihar Enugu, Dakta Dan Shere da wasu adadin mutanen da har zuwa yanzu ba a san adadinsu ba. 

An nakalto cewa, Mista Dan na daga cikin matafiya da dama da aka yi garkuwa da su a kan hanyar Enugu-Ugwuogo zuwa Nike-Nsukka a ranar Alhamis.

  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Mutum Da Katin Zabe Sama Da 100 A Sakkwato 
  • Kisan Kai: Kwamishinan ‘Yansanda Ya Bada Umarnin Yin Bincike Kan Mutuwar Jami’in Dansanda A Kebbi

Dakta Dan ya yi aiki ne a karkashin gwamnatin gwamna Chimaroke Nnamani.

LEADERSHIP ta rawaito cewa, Shere, kwararren likita ne, ya yi tafiya ne zuwa Nsukka domin halartar ganawa a yayin da ya ci karo da ‘yan bindigar da suka farmakesu shi da sauran matafiya.

Majiyoyi sun ce ‘yan bindigar da yawansu ya haura takwas ne suka kaddamar da wannan harin, kuma sun yi ta harbe-harbe kafin daga bisani su sace mutanen.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

“Sun yi ta harbin motocinmu; daya daga cikinmu ma harsashi ya same shi. Amma direbanmu ya yi kokari ya arce. Mun samu nasarar kai wanda aka harba zuwa asibiti,” a cewar daga daga cikin fasinjojin da suka tsira.

A wani labarin makamancin wannan, wasu ‘yan bindiga da suka yi garkuwa da mutane a ranar Lahadi suna ta kara kudin karbar fansa.

“Da farko sun nemi diyyar miliyan biyu na mutum daya daga cikin wadanda suka sace, amma daga baya suka sauya farashi, yanzu kuma sun kara har zuwa miliyan 30.

“Sun yi ta binciken wayoyin wadanda suka sace din ne domin gano ko su waye da irin girmansu,” a cewar majiya.

Sannan, daliban Jami’ar Nijeriya da ke Nsukka da aka yi garkuwa da su a ranar Lahadi har yanzu suna tsare a hannun masu garkuwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GarkuwaTsohon Sakataren Gwamnatin EnuguYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manufar Sin Ta Fadada Bude Kofa Ga Waje Za Ta Tallafawa Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Xi Ya Taya Murnar Shirya Bikin Liyafar Shekara-Shekara Ta Kwamitin Huldar Amurka Da Sin

Related

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya
Da ɗumi-ɗuminsa

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

1 week ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

2 weeks ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

3 weeks ago
Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

4 weeks ago
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita
Da ɗumi-ɗuminsa

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita

1 month ago
Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu
Da ɗumi-ɗuminsa

Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu

2 months ago
Next Post
Xi Ya Taya Murnar Shirya Bikin Liyafar Shekara-Shekara Ta Kwamitin Huldar Amurka Da Sin

Xi Ya Taya Murnar Shirya Bikin Liyafar Shekara-Shekara Ta Kwamitin Huldar Amurka Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Taron Kolin ASEAN: Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci

Taron Kolin ASEAN: Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci

May 28, 2025
Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice

Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice

May 28, 2025
Mutum 1 Ya Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Mummunan Hatsarin Mota A Abuja

Mutum 1 Ya Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Mummunan Hatsarin Mota A Abuja

May 28, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai

Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai

May 28, 2025
Unity Cup: Yau Nijeriya Da Ghana Zasu Kece Raini A Birnin Landan

Unity Cup: Yau Nijeriya Da Ghana Zasu Kece Raini A Birnin Landan

May 28, 2025
Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci

Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci

May 28, 2025
Kotu Ta Ci Tarar  El-Rufai Miliyan 900 Saboda Wani Laifi Da Ya Yi A 2019

Kotu Ta Ci Tarar  El-Rufai Miliyan 900 Saboda Wani Laifi Da Ya Yi A 2019

May 28, 2025
An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

May 27, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wani Ɗan Bindiga, Sun Ƙwato Makamai Bayan Artabu A Taraba

May 27, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka

May 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.