ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kisan Kai: Kwamishinan ‘Yansanda Ya Bada Umarnin Yin Bincike Kan Mutuwar Jami’in Dansanda A Kebbi

by Umar Faruk
4 years ago
'Yansanda

Kwamishinan ‘yansandan Jihar Kebbi, CP Ahmed Magaji-Kontagora, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan al’amuran da suka faru na mutuwar ASP Shu’aibu Sani Mulunfashi.

Hakan na kunshe ne a cikin wata takardar manema labarai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansanda DSP Nafi’u Abubakar kuma aka rabawa manema labarai a Birnin Kebbi.

  • Barazanar Harin Abuja: ‘Yan Ta’adda Ba Sa Bayyana Lokaci Da Wurin Kai Hari – Shehu Sani 
  • Da Dumi-Dumi: Bankin CBN Zai Sake Sauya Fasalin Naira N200, N500 Da N1,000

Wanda a ranar 19 ga Oktoba, 2022 da misalin karfe 2:10 na rana , wani ASP Abdullahi Garba, jami’in ‘yan sanda na Sauwa, ya samu sabani da ASP Shu’aibu Sani Malunfashi, jami’in sashen binciken aikata laifuka na II, hedikwatar ‘yan sanda ta Argungu, a wajen kamun kifi na garin Argungu. A dalilin haka ne suka yi artabu da juna a gaban shagon ASP Abdullahi Garba.

ADVERTISEMENT

A yayin da ake fafatawa, ASP Abdullahi Garba ya yi amfani da almakashi ya daba wa ASP Shu’aibu Sani Malunfashi a hakarkarinsa na hagu. Da samun rahoton, jami’in ‘yan sanda na Argungu, sun garzaya wurin da lamarin ya faru, inda suka damke jami’in da ya aikata laifin.

Bisa ga hakan ne aka garzaya da ASP Shu’aibu Sani Malunfashi zuwa Asibitin tunawa da Sarki Yahaya da ke Birnin Kebbi, inda Likita ya tabbatar da mutuwarsa.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Sakamakon haka, jami’in ‘yan sanda da ya aikata laifin, ASP Abdullahi Garba, aka tsare shi a sashin binciken manyan laifuka na jihar da ke Birnin Kebbi, yayin da kuma aka mika binciken nasa zuwa sashin kisan kai domin gudanar da bincike mai zurfi don gano musababbin lamarin.

Kazalika, Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Kebbi ya aike da tawagar manyan jami’an ‘yan sanda domin ta’aziyya ga ‘yan uwa da abokan arziki wanda ya rasu tare da addu’ar Allah ya jikan Asp Shu’aibu Sani Malunfashi ya gafarta masa.

Bugu da Kari CP Ahmed Magaji Kontagora ya kuma yi Allah-wadai da matakin da jami’in da ya yi kuskure ya nuna wanda ya saba wa koyarwar ‘yan sanda da dokar ‘yan sanda da kuma sauran dokokin da suka shafi kundin kasar Nijeriya.

Hakazalika, CP ya gargadi jami’an rundunar da su zauna lafiya a kodayaushe tare da kai rahoton korafe-korafen su ga sassan da suka dace a cikin rundunar domin gyara a maimakon daukar doka ga hannu.

Daga karshe kwamishinan ya tabbatar wa da jama’a cewa, za a yi adalci wajen gudanar da bincike kan lamarin sannan kuma za a bayyana sakamakon binciken.

'Yansanda
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Jarin Ketare Da Aka Zuba Kai Tsaye A Kasar Sin Ya Haura Yuan Triliyan 1 Daga Janairu Zuwa Satumba

Jarin Ketare Da Aka Zuba Kai Tsaye A Kasar Sin Ya Haura Yuan Triliyan 1 Daga Janairu Zuwa Satumba

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.