ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kisan Kai: Kwamishinan ‘Yansanda Ya Bada Umarnin Yin Bincike Kan Mutuwar Jami’in Dansanda A Kebbi

by Umar Faruk
4 years ago
'Yansanda

Kwamishinan ‘yansandan Jihar Kebbi, CP Ahmed Magaji-Kontagora, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan al’amuran da suka faru na mutuwar ASP Shu’aibu Sani Mulunfashi.

Hakan na kunshe ne a cikin wata takardar manema labarai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansanda DSP Nafi’u Abubakar kuma aka rabawa manema labarai a Birnin Kebbi.

  • Barazanar Harin Abuja: ‘Yan Ta’adda Ba Sa Bayyana Lokaci Da Wurin Kai Hari – Shehu Sani 
  • Da Dumi-Dumi: Bankin CBN Zai Sake Sauya Fasalin Naira N200, N500 Da N1,000

Wanda a ranar 19 ga Oktoba, 2022 da misalin karfe 2:10 na rana , wani ASP Abdullahi Garba, jami’in ‘yan sanda na Sauwa, ya samu sabani da ASP Shu’aibu Sani Malunfashi, jami’in sashen binciken aikata laifuka na II, hedikwatar ‘yan sanda ta Argungu, a wajen kamun kifi na garin Argungu. A dalilin haka ne suka yi artabu da juna a gaban shagon ASP Abdullahi Garba.

ADVERTISEMENT

A yayin da ake fafatawa, ASP Abdullahi Garba ya yi amfani da almakashi ya daba wa ASP Shu’aibu Sani Malunfashi a hakarkarinsa na hagu. Da samun rahoton, jami’in ‘yan sanda na Argungu, sun garzaya wurin da lamarin ya faru, inda suka damke jami’in da ya aikata laifin.

Bisa ga hakan ne aka garzaya da ASP Shu’aibu Sani Malunfashi zuwa Asibitin tunawa da Sarki Yahaya da ke Birnin Kebbi, inda Likita ya tabbatar da mutuwarsa.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Sakamakon haka, jami’in ‘yan sanda da ya aikata laifin, ASP Abdullahi Garba, aka tsare shi a sashin binciken manyan laifuka na jihar da ke Birnin Kebbi, yayin da kuma aka mika binciken nasa zuwa sashin kisan kai domin gudanar da bincike mai zurfi don gano musababbin lamarin.

Kazalika, Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Kebbi ya aike da tawagar manyan jami’an ‘yan sanda domin ta’aziyya ga ‘yan uwa da abokan arziki wanda ya rasu tare da addu’ar Allah ya jikan Asp Shu’aibu Sani Malunfashi ya gafarta masa.

Bugu da Kari CP Ahmed Magaji Kontagora ya kuma yi Allah-wadai da matakin da jami’in da ya yi kuskure ya nuna wanda ya saba wa koyarwar ‘yan sanda da dokar ‘yan sanda da kuma sauran dokokin da suka shafi kundin kasar Nijeriya.

Hakazalika, CP ya gargadi jami’an rundunar da su zauna lafiya a kodayaushe tare da kai rahoton korafe-korafen su ga sassan da suka dace a cikin rundunar domin gyara a maimakon daukar doka ga hannu.

Daga karshe kwamishinan ya tabbatar wa da jama’a cewa, za a yi adalci wajen gudanar da bincike kan lamarin sannan kuma za a bayyana sakamakon binciken.

'Yansanda
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Jarin Ketare Da Aka Zuba Kai Tsaye A Kasar Sin Ya Haura Yuan Triliyan 1 Daga Janairu Zuwa Satumba

Jarin Ketare Da Aka Zuba Kai Tsaye A Kasar Sin Ya Haura Yuan Triliyan 1 Daga Janairu Zuwa Satumba

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.