• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: ‘Yansanda Sun Cafke Dakataccen Kwamishinan Zaben Adamawa, Ari 

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Da Dumi-Dumi: ‘Yansanda Sun Cafke Dakataccen Kwamishinan Zaben Adamawa, Ari 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Nijeriya (NPF) ta cafke Barista Hudu Yunusa-Ari, dakataccen kwamishinan hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa a jihar Adamawa (REC) domin fuskantar tuhume-tuhume.

 

A wata sanarwar da ‘yansanda suka fitar a ranar Talata dauke da sanya hannun Kakakin hukumar, CSP Olumuyiwa Adejobi, ya ce, Yunusa-Ari dai ya shiga hannun tawagar ‘yansanda na sashin tsare-tsare, bibiya da sa-ido kan harkokin zabe ne a ranar Talata a Abuja.

  • Majalisar Dokokin Adamawa Ta Tabbatar Da Mace Ta Farko Babban Jojin Jihar

CSP Adejobi ya ce, yanzu haka Hudu yana karkashin kulawar ‘yansanda kuma za su masa tulin tambayoyi dangane da tataburza da kuma dalilan da suka janyo aka gudanar da wasu abubuwan da ba na daidai ba a lokacin kammala zaben gwamnan Jihar Adamawa kwanakin baya.

 

Labarai Masu Nasaba

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Ya ce, “Su ma sauran jami’ai da daidaikun da suke da hannu a lamarin su na nan su na fuskantar tambayoyin jami’an.

 

“Sufeto-janar na ‘yansanda ya bada tabbacin cewa dukkanin wani ko wasu da ke da hannu a lamarin to tabbas za a tuhume shi/su har ma a gurfanar da su kamar yadda yake kunshe a kundin tsarin da doka ya tanadar,” a cewar FPRO.

 

Idan za a tuna dai Ari ya ayyana cewa Sanata Aisha Binani ce ta lashe zaben gwamnan Jihar amma bai bayyana adadin kuri’un da ta lashe zaben a lokacin ba, lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce. Daga baya kuma INEC ta ce ba a bi ka’ida ba don haka aka soke wannan tare da ayyana gwamna mai ci a jihar, Ahmadu Fintiri a matsayin wanda ya lashe zaben.

 

Kodayake Ari ya fito ya ce shi kam ya nan kan bakarsa domin ya yi amfani da tsarin doka ne wajen ayyana Binani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Za Ta Karfafa Kare Namun Daji Karkashin Sabuwar Dokar Da Aka Kaddamar

Next Post

Rundunar ‘Yan Sanda Sun Cafke Dan Yahoo Da Ya Kware Kan Cutar ‘Yan Kasar Hungary A Nijeriya

Related

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano
Labarai

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

2 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

4 hours ago
bakin wake
Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

6 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar
Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

8 hours ago
Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

10 hours ago
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Labarai

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

10 hours ago
Next Post
Rundunar ‘Yan Sanda Sun Cafke Dan Yahoo Da Ya Kware Kan Cutar ‘Yan Kasar Hungary A Nijeriya

Rundunar 'Yan Sanda Sun Cafke Dan Yahoo Da Ya Kware Kan Cutar 'Yan Kasar Hungary A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

June 1, 2025
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

June 1, 2025
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.