• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Farko Na Ji Kamar Ba Zan Iya Ci Gaba Da Harkar Fim Ba —Umar Faruk

by Rabi'at Sidi Bala
3 years ago
in Nishadi
0
Da Farko Na Ji Kamar Ba Zan Iya Ci Gaba Da Harkar Fim Ba —Umar Faruk
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon Jarumi me shirin zama babba anan gaba, wanda ya bayyana a masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, kuma daya daga cikin Jaruman da suka taka rawa a cikin shirin Malamin Kauna.

UMAR FARUK ABUBAKAR wanda aka fi sani da UMAR FARUK NE, ya shiga masana’antar Kannywood da zafinsa, inda ya shirya wani kayataccen shiri me dogon zango wanda masu kallo ke jiran isowarsa gare su, shiri me suna AMARYAR SHEKARA.

  • Yadda Ake Cin Gajiyar ‘Google Drive’ Wajen Amfani Da Kwanfuta
  • An Yi Atisayen Karshe Na Dukkan Fannoni Don Share Fagen Karbar Kumbon Shenzhou-14

Jarumin ya bayyana wa masu karatu irin kalubalen daya fuskanta tun kafin shigarsa cikin masana’antar, kuma ya yi kira ga masu kallo, da masu kokarin shiga cikin masana’antar har ma da wadanda ke ciki. Ga dai tattaunawar tare da wakiliyarmu RABI’AT SIDI BALA kamar haka.

Masu karatu za su so su ji cikakken sunanka tare da sunan da aka fi saninka da shi.

Sunana Umar Faruk Abubakar Sadeek wanda aka fi sani da Umar Faruk Ne.

Labarai Masu Nasaba

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Me ya sa ake kiranka da Umar Faruk Ne, ganin yadda aka kara Ne?

Umar Faruk Ne ya samo asali ne ta dalilin wani abokina, shi yake fada min, saboda akwai masu suna Umar Faruk da yawa kuma masana’antar mu daya.

Ko za ka fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinka?

An haife ni a Jihar Yobe karamar hukumar Gulani, sunan garin mu BUMSA. Na yi karatun addini dai-dai gwargwado, sannan na yi karatun boko in da na dakata a iya Sakandare. A yanzu haka na yi aure ina tare da matata guda daya.

Ya batun ci gaba da karatu, shin za a ci gaba ko iya nan ya wadatar?

Komai nufi ne na Allah, amma dai muna sa ran ci gaba in sha Allah.

Me ya ja hankalinka har ka tsunduma cikin masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood?

Abun da ya ja hankalina yadda na ga ‘yan fim suna tura sakonninsu kuma sakonnin suna Isa kai tseye.

Wanne rawa kake takawa a cikin masana’antar?

Ina taka rawa matsayin Jarumi.

Za ka yi kamar shekara nawa da fara fim?

Eh! to ban wani dade sosai ba, ba zan fi shekara guda ba, kasancewar da waka nake lokacin ina zaune a Abuja.

Idan na fahimce ka kana so ka ce, bayan harkar fim har waka kana yi kenan?

Eh! Ina waka amma yanzu na fi bawa fim karfi.

Kafin mu je ga wakar, shin ya gwagwarmayar shiga masana’antar ta kasance, musamman yadda wasu ke kuka ga samun shigarta?

Na sha gwagwarmaya sosai kafin kasancewa ta cikin harkar, amma cikin ikon Allah mutum 2 ne silar shiga ta, wanda ba zan taba macncewa da su ba kome na zama.

Ya farkon farawar ka ya kasance, musamman yadda kake sabo a lokacin?

Na ji kamar ba zan iya ba, zuciya ta har sake-sake take min.

A wanne fim ka fara fitowa?

Na fara fitowa a fim din ‘Malamin Kauna’.

Kai ka ja fim din ko wani ne daban?

A’a! ba ni bane ina dai ciki daga wani bangaren daban.

Wanne waje ne ya fi baka wahala a cikin shirin?

Wani ‘scene’ ne muka yi da wani Jarumi har ce min yake in kwantar da hankalina, yana karamin karfin gwiwa.

Ko akwai wani kalubale daka samu daga wajen iyayenka, musamman lokacin da ka fara zuwar musu da labarin kana son shiga masana’antar?

Sosai ma dan sai da nayi kamar in hakura, amma sai na yi wa wani yayana bayani sosai ya fahimce ni, sannan shi ma sai ya yi wa mahaifiyarmu bayani ta fahimce shi, sannan aka bar ni.

Ya ka ji a lokacin da burinka ya cika?

Na ji farin ciki saboda burina ya cika na samu nasara.

A baya ka fadi cewa ka fara fitowa a cikin shirin ‘Malamin Kauna’, wanne rawa ka taka cikin shirin?

Rawar da na taka ita ce; duk wani wanda yake da matsala kowacce kala ce, idan ya same ni toh! takau matukar zai biya ni.

Daga lokacin da ka fara kawo iyanzu kayi fim sun kai kamar guda nawa?

Eh! ba su da yawa yawanci masu dogon zango ne, na yi fim za su kai kamar guda bakwai.

Ko za ka iya fadowa masu karatu sunayen wasu daga ciki?

Eh! Sosai ma, ga wasu faga ciki, akwai “Malamin Kauna, Akasi, Bawan Allah, Burin Asabe, Amaryar Shekara” da sauransu.

Duk sun fita ko kuma suna kan hanyar fita?

Eh! toh, wasu sun fita wasu kuma suna kan hanyar fita kamar dai Amaryar shekara da zai fita a ranar laraba 30/11/22, in sha Allah.

A gaba daya fina-finan da ka fito ciki,wanne fim ne ya fi kwanta maka a rai, wanda ya zama bakandamiyarka, wanda ka fi so ya fi shiga ranka, kuma me yasa?

Gaskiya a fina-finan dana fito ciki na fi son Amaryar Shekara. Ina son fim din sabida yadda labarin ya tsaru kuma shi din mallakina ne.

Kana so ka ce Amaryar Shekara kai ka shirya shi, ka dauki nauyin shirin?

Eh! kwarai kuwa gaba dayansa nawa ne, ni na dauki nauyinsa tun daga kan labarin da shiryawa da duk abin da dai ya shafi shirin ni na dau nauyi. Amma wanda ya rubuta labarin Abba Harara, wanda ya bada Umarni Ibrahim Bala.

Me fim din ke kunshe da shi, wanne sako ake son isarwa ga al’umma?

Sako ne da ake son isarwa akan masu yin auren kisan wuta,wanda suke aure akan wani wa’adi.

Shi wannan shiri na ‘Amaryar Shekara’ takaitaccen labari ne ko me dogon zango?

A’a! Me dogon zango ne, ba takaitacce bane.

Ya kake kallon yadda karbuwar fim din zai kasance ga su masu kallon, kana ganin kwalliya za ta biya kudin sabulu kuwa?

In sha Allahu, haka nake ji a raina, kwalliya za ta biya kudin sabulu, domin shiri ne daya samu ingantaccen aiki.

Kamar wadanne Jarumai ne suka fito cikin shirin?

Suna da yawa irin su; Salisu S. Fulani, Ibrahim Bala, Nasir Naba, Diamond Zahra, Momy Niger da sauransu.

Wanne iriin kalubale ka taba fuskata game da harkar fim tun daga farkon farawarka kawo iyanzu?

Gaskiya ni dai ban san ko nan gaba ba, amma a yandu ba wani kalubale.

Game da Nasarori fa wanne irin Nasarori ka samu?

Na cinma nasarori da dama.

Ya ka dauki fim a wajenka?

Na dauki fim sana’a, sannan kuma hanyar tura sako ga al’umma.

Me kake son cimma game da fim?

Suna da dama ai ina so in taimaki kaina game da ‘yan uwana da duk wani wanda muka alakantu da shi ko ta nesa ne.

Ko kana da Ubangida a cikin masana’antar?

Eh! Ina da shi, Ali Rabiu Ali Daddy

Wane ne babban abokinka a cikin masana’antar Kannywood?

Babban abokina shi ne; Abba Harara.

Ya alakarka take ada da kuma yanzu tsakaninka da sauran abokanka na baya?

Har yanzu babu abin da ya canza, wanda muke wasa da su har yanzu ba mu daina ba.

Bayan harkar fim kana wata sana’ar ne, idan kana yi wacce sana’a ce kuma ya kake iya hada harkar fim dinka da kuma sana’arka?

Eh! Ina wata sana’ar, ko wanne baya shafar kowanne, saboda bana sana’ar wuni guri daya ‘online business’ nake.

Da wanne Jarumi kafi son a hada ka fim da shi?

Ina so a hada ni fim da Salisu S Fulani. Abin da ya sa kuwa shi ne; Matsayina na sabon Jarumi da muka yi aiki da shi ya bani shawarwari sannan da kwarin gwiwa.

Wanne abu ne ya taba faruwa da kai na farin cii ko akasin haka wanda ba za ka taba mantawa da shi a rayuwarka ba?

Eh! abun farin ciki shi ne; Ranar Aure na.

Wanne irin abinci da abin sha ka fi so?

Na fi son Shinkafa da Miya.

Wanne irin kaya ka fi son sakawa?

Na fi son Shadda.

Matsayinka na sabon Jarumi mene burinka anan gaba game da harkar fim?

Na zama babban jarumi wanda duniya take alfahari da shi.

Kafin ka fara fim ko akwai fim din daya taba burgeka, wanda har ya taba maka zuciya da har ka ji da ma a ce kai ne ciki, kuma wanne Jarumi ne gwaninka?

Abdul M Shareef shi ne Jarumi na, sannan fim dinshi ne ya fara birge ni na ji ina so in kasance ni ma daya daga cikinsu. ‘Jani Muje’ an yi abubuwa da yawa wanda suka birge ni a ciki.

Wacce shawara za ka bawa sauran abokan aikinka da suke cikin harkar har ma da wadanda suke kokarin shiga?

Mu rike amanar juna ban da yada aibun ‘yan uwanmu sannan mu daraja juna. ‘Yan baya kuma ina me kara musu kwarin guiwa.

Ko akwai wani kira da za ka yi ga gwamnati game da harkar fim?

Ya kamata gwamnati ta rinka shiga cikin lamuranmu, domin muna da mahimmin rawa da muke takawa a kasa.

Wanne kira kake da shi ga masu kallo?

Ina kira ga masu kallon fina-finan mu da su dinga yi mana adalci gurin fassara mu.

Me za ka ce da wannan shafi na Rumbun Nishadi, har ma da ita kanta Jaridar LEADERSHIP Hausa?

Ina yi wa wannan shafi fatan alheri a ko da yaushe, Allah ya kara daga darajarsu sama.

Ko kana da wadanda za ka gaisar?

Ina mika gaisuwa ta musamman ga masoyana na fadin duniya.

Muna godiya

Ni ma na gode.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FitowaJarumiKannywoodNishadiRawaUmar Faruk
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kalaman Kiyayya Da Yada Su Na Haddasa Rikici Tsakanin Al`umma

Next Post

Da Gaske Soyayya Yankin Azaba Ce?

Related

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

6 days ago
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
Nishadi

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

2 weeks ago
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
Nishadi

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

2 weeks ago
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna
Nishadi

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

2 weeks ago
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ
Nishadi

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

3 weeks ago
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami
Nishadi

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

3 weeks ago
Next Post
Da Gaske Soyayya Yankin Azaba Ce?

Da Gaske Soyayya Yankin Azaba Ce?

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.