• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Me Nijeriya Za Ta Iya Amfana A Zaben Amurka?

by Bilkisu Tijjani and Sulaiman
11 months ago
in Taskira
0
Yadda Donal Trump Ya Lashe Zaben Shugabancin Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wane darasi ‘yan Nijeriya suka dauka akan kama yaran da aka yi a lokacin Zanga-zanga?

 

Shafin Taskira shafi ne da ya saba zakolo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma. Tsokacimmu na yau zai yi duba ne game da zaben Amurka da kama yara da aka yi a lokacin zanga zanga akan tsare su.

 

Fatima Abdullahi.

Labarai Masu Nasaba

Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

Bukatar Mutane Su Kula Da Warin Jikinsu

‘yan Nijeriya za su iya amfana ta hanya dimokaradiyya da hanyar zaman lafiya da sasanci, muna sa ran wannan zaban da aka yi na Amurika ya kawo mana cigaba da zaman lafiya a kasarmu Nijeriya da sauran kasashe baki daya.

 

‘Yan Nijeriya sun dauki darasi akan yaran da aka kama lokacin zanga-zanga saboda sun sha wahala an kulle su a Abuja ba ci ba sha, daga karshe wasu daga cikinsu har faduwa suke saboda yunwa. Sai da shugaban kasa ya shiga maganar ya ce a sake su, to gaskiya wanan darasi ne babba da ya kama ta mu dauka kuma mu kiyaye gaba, zama da yunwa ba shi da dadi sannan an dauke ka cikin ‘yan uwanka kana can wani gari kana rayuwa ta kunci da azaba, iyaye sun shiga tashin hankali saboda ba su san halin da ‘ya’yansu ke ciki ba, da sun kasa bacci sun kasa ci da sha saboda fargaba ba su san halin da ‘ya’yansu suke ciki ba, suna raye ba sa raye su dai suna ta addu’a ne. Da wannan nake fadakar da iyaye da kuma ‘yan uwa da mu kiyaye gaba akan wannan lamari. Allah ya kiyaye gaba.

 

Hassan Tijjani

Wannan zabe da aka yi na Amurka muna sa ran ya kawo mana karfin Dimokaradiyya, da sanya muradin ci gaban kasa a kan kowane abu kamar yadda ‘yar takarar shugabancin kasar ta yi tawakkali da hukuncin zabe, ba tare da ta da hankali, ko kalubalantar hukunci a kotu ba.

 

Wannan kama ‘yan Nijeriya da aka yi muna sa ran ya kawo mana karfin hadin kai, tare da yin murya daya a kowane lokaci don cinma bukata.

 

Sannan kuma muma talakawa mu kiyaye duk abin da akace an sa masa doka to mu yi kokarin bin dokar shugabanni kar mu kuskura mu kusanci yin wannan abin ballantana har ya kai ga an kama mu, bin shugabanni ya zama dole ba wai su za mu duba ba, fadin Allah za mu duba bin shuwaganni shi ne bin Allah, su kuma idan sun yi adalci a kanmu sun gyautawa kansu idan ba su yi ba kansu suka yi wa, ko badade ko bajima zai dawo musu.

 

Habiba Tijjani

‘Yan Nijeriya za su iya amfana da zaben Amurka ta hanya dimokaradiyya, sannan ta hanyar shawarwari a tsakanin shuwagabannin guda biyu ta bangaren zaman lafiya da tsaro tun da shi shugaban da ya ci zaben na yanzu na Amurka ana gani shi ba me son tashin hankali bane yana son zaman lafiya, to muna sa ran samun zaman lafiya a duniya baki daya. Sannan ta hanyar cinikayya saboda shi ana ganin dan kasuwa ne to za mu iya amfana ta haka.

 

‘Yan Nijeriya ya kamata mu dauki darasi akan abin da ya faru da ‘yan uwammu na kama su da aka yi, wasu suna ganin ba su da laifi wasu kuma suna gani bai kamata a kama su ba, saboda ko suna da laifi shekarunsu ba su kai a kama su ba, to saboda haka da hukuma sun yi hakuri sun bar su tun da shekarunsu bai isa a musu hukunci ba.

 

To ya kamata ‘yan Najeriya su kiyaye su kuma guji gaba kada irin haka ta kara faruwa. Allah yasa mu dace.

 

Bilkisu Sani Amar

Assalamu alaikum. Darasin da ‘yan Nijeriya suka dauka akan kama ‘yan Nijeriya da aka yi a lokacin zanga-zanga, ya nuna hali irin na ‘yan siyasa don su nuna kyautatawa da aka yi masu don kada a zarge su ba don komai ba, kuma wannan ba zai hana a sake yin zanga-zangar ba, domin har yanzu gwamnatin Tinubu ba ta rage karin man fetur din da aka yi ba sai ma karawa da aka sake yi, saboda haka duk siyasa ce kawai dama a haka suka yi aka zabe su domin zuwa da suka yi kauyuka suka raba kayan abinci don a zabe su kamar abin arziki ashe abin tsiya ne siyasa ta zama yaudara a kasar Nijeriya domin suna yi wa kansu ne ba jama’a ba, domin da suna yi ne don kishin kasa to da ba za a samu yaudara ba, sanadiyyar karin kudin mai ya haddasa matsaloli da dama da suka hada da tsadar kayayyakin masarufi da suka hada da tsadar kayan abinci, kayan sawa wato sutura dadai sauransu. Muna fatan zabe na ga ba Allah ya zaba mana shugabanni nagari


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kaddamar Da Tsarin Taswirar Sinanci Da CMG Ya Baiwa Dakin Adana Kayan Tarihin Larco Na Peruø

Next Post

Xi Ya Halarci Kwarya-Kwaryar Taron Shugabannin APEC Karo Na 31 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Related

Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu
Taskira

Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

1 day ago
Bukatar Mutane Su Kula Da Warin Jikinsu
Taskira

Bukatar Mutane Su Kula Da Warin Jikinsu

1 week ago
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari
Taskira

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

1 month ago
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi
Taskira

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

3 months ago
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu
Taskira

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

3 months ago
Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo
Taskira

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

4 months ago
Next Post
Xi Ya Halarci Kwarya-Kwaryar Taron Shugabannin APEC Karo Na 31 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Ya Halarci Kwarya-Kwaryar Taron Shugabannin APEC Karo Na 31 Tare Da Gabatar Da Jawabi

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.