ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Halarci Kwarya-Kwaryar Taron Shugabannin APEC Karo Na 31 Tare Da Gabatar Da Jawabi

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Xi

A ranar 16 ga wannan wata agogon kasar Peru, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya isa cibiyar taro ta Lima domin halartar kwarya-kwaryar taron shugabannin APEC karo na 31, tare da gabatar da wani muhimmin jawabi.

 

Cikin jawabinsa, Xi ya yi nuni da cewa, a halin yanzu, ana yin manyan sauye-sauye a duk fadin duniya, domin tattalin arzikin duniya bai samu ci gaba yadda ya kamata ba, kuma an gamu da matsala yayin bude kofa ga wasu, sannan hadin gwiwar dake tsakanin kasashen yankin Asiya da tekun Pasifik shi ma yana fama da kalubale.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Bauchi Ta Kaddamar Da Kwamitin Adana Kayan Abinci
  • An Yi Bikin Kaddamar Da Shirin Zababbun Kalaman Shugaba Xi Jinping “Zango Na 3” Da Harshen Sifaniya A Peru

A don haka shugaban ya ce, ya dace kasashen yankin su hada kai domin tabbatar da muradun Putrajaya nan da shekarar 2040 da shugabannin APEC suka fitar a shekarar 2020, da karfafa gina kyakkyawar makomar bai daya ta al’ummun kasashen yankin Asiya da tekun Pasifik, tare kuma da kafa sabon zamani na ci gaban yankin.

 

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Daga baya shugaba Xi ya gabatar da shawarwari uku, na farko, kafa tsarin hadin gwiwa ba tare da rufa-rufa ba tsakanin kasashen yankin. Ya ce, kasar Sin tana nacewa kan manufar aiwatar da tsare-tsaren RCEP, da CPTPP, da DEPA, haka nan tana son tattaunawa da bangarorin da abin ya shafa kan cinikayya a fannonin fasahar zamani da kare muhalli, tare kuma da kara habaka yankunan cinikayya marasa shinge zuwa matakin koli a fadin duniya.

 

Na biyu, neman samun sabon kuzarin kere-kere a yankin Asiya da tekun Fasifik, inda kasar Sin za ta fitar da “Shawarar hadin gwiwa kan musayar alkaluma tsakanin kasashen duniya”, domin zurfafa hadin gwiwa tsakaninta da sauran kasashen duniya a bangaren.

 

Na uku, tsara tunanin raya yankin Asiya da tekun Fasifik da zai haifar da alfanu ga kowa da kowa, yayin da a nata bangaren, kasar Sin za ta yi kokari domin kara kudin shigar al’ummun kasashen mambobin kungiyar APEC, da daukaka ci gaban matsakaita da kananan masana’antu, da habaka ci gaban tattalin arziki a yankin Asiya da tekun Pasifik.

 

Ban da wannan kuma, Xi ya sanar da cewa, kasar Sin ce za ta karbi bakuncin kwarya-kwaryar taron da shugabannin kungiyar hadin gwiwar tattalin arziki ta yankin Asiya da teku Fasifik APEC za su gudanar a shekarar 2026. Ya bayyana cewa, kasarsa tana maraba da kuma tsumayar aiki tare da dukkan bangarorin da abin ya shafa wajen zurfafa hadin gwiwar yankin Asiya da tekun Fasifik domin amfanar da al’ummomin manyan yankunan guda biyu. (Mai fassara: Jamila)

Xi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30
Xi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka
  • Sulaiman
    Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen
  • Sulaiman
    Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya
  • Sulaiman
    2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

MASU ALAKA

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?
Daga Birnin Sin

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Next Post
MOFA: Kasar Sin Na Son Sanya Sabon Kuzari A Ci Gaban Tattalin Arzikin Yankin Asiya Da Tekun Fasifik Da Ma Duniya

MOFA: Kasar Sin Na Son Sanya Sabon Kuzari A Ci Gaban Tattalin Arzikin Yankin Asiya Da Tekun Fasifik Da Ma Duniya

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026  Mrs Zubaida Umar

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar

September 11, 2026
Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

September 11, 2026
Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

September 11, 2026
Sanata yari

Gwarzon Ɗan Siyasa Na Shekarar 2026 Sanata Abdul’Aziz Abubakar Yari

September 11, 2026
Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.