• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Sa Hannun Gwamnatin Zamfara ‘Yan Daba Suka Farmake Mu – Dan Takarar Gwamna A PDP

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
3 years ago
in Siyasa
0
Da Sa Hannun Gwamnatin Zamfara ‘Yan Daba Suka Farmake Mu – Dan Takarar Gwamna A PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗan takarar Gwamnan Jihar Zamfara a jam’iyyar PDP, Dakta Dauda Lawal, ya yi tir da harin da wasu ‘yan daba suka kai kan tawagarsa wanda ya yi zargin cewa gwamnatin jihar, ƙarƙashin gwamna Matawalle ce ta ɗauki hayarsu don su aiwatar da hakan.

Ya misalta harin a matsayin kololuwar karya doka da oda tare da neman haifar da hatsaniya da tashin hankali a jihar.

  • Zamfarawa Na Alfahari Da Sadiya Umar Farouq – Gwamna Matawalle

Lawal a wata sanarwar da cibiyar yaɗa labaransa ta fitar a ranar asabar a Gusau, ya ce, wasu ‘yan daba ɗauke da muggan makamai sun kai musu harin ne a daren ranar juma’a a lokacin da suke kan hanyar shiga Gusau, babban birnin Jihar Zamfara.

Sanarwar ta nuna lamarin a matsayin abin kaico, takaici da damuwa, “An san PDP da mutunta doka da oda, mu jam’iyya ce da muka dukufa wurin gudanar da harkokinmu kan doka da oda. Wannan dalilin ne ma ya sanya sai da muka jira hukumar zaɓe (INEC) ta bada damar gudanar kamfen ɗin gwamna kafin mu shirya wani taron siyasa a jihar Zamfara.

“PDP ta sanya ranar 15 ga watan Oktoba domin ta amshi dubban waɗanda suka sauya sheƙa daga APC zuwa PDP, tare da ƙaddamar da kwamitin yaƙin zaɓen gwamna na 2023.

Labarai Masu Nasaba

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

“Yan daban da Jam’iyyar APC da Gwamna Matawalle suka ɗauko hayarsu ne suka farmaki tawagarmu a kan hanyarmu ta zuwa Gusau. Motocinmu da dama an lalata, tare da kona wasu a yayin harin.

“A yau kuma ‘yan daban a ƙarƙashin wani Aliyu Alhazai Shinkafi, tsohon Shugaban kwamitin yaki da daba, kuma shugaban hukumar kula da cinkoson ababen hawa (ZAROTA) suka farmaki gidan dan takarar Gwamna na jam’iyyar PDP.

“Wannan sabon harin abun kaico ne inda aka kai hari kan motocin yaƙin zabenmu tare da sace duk wani abu mai muhimmanci a cikinta.

“Mun sani APC da Gwamnatin Matawalle za su iya yin komai domin kawo cikas ga harkokin siyasa da yaƙin zaɓenmu.”

Sanarwar ta bukaci Shugaban ‘yan sanda na ƙasa da sauran hukumomin tsaro da su kaddamar da bincike kan lamarin tare da shigowa cikin batun don kauce wa shigar da jama’a cikin firgici da tashin hankali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan-Adam Da Ake Iya Sarrafa Shi Daga Nesa

Next Post

An Bude Babban Taron Wakilan JKS Karo Na 20

Related

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

10 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Manyan Labarai

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

11 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

1 day ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Siyasa

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

3 days ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

4 days ago
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC
Labarai

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

4 days ago
Next Post
An Bude Babban Taron Wakilan JKS Karo Na 20

An Bude Babban Taron Wakilan JKS Karo Na 20

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

July 11, 2025
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.