ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfarawa Na Alfahari Da Sadiya Umar Farouq – Gwamna Matawalle

by Sulaiman
4 years ago
Farouq

Gwamna Bello Muhammed Matawalle na Jihar Zamfara ya bayyana Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, a matsayin nagatartacciyar ‘yar jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne kwanan nan a wajen ƙaddamar da shirin ba da tallafin kuɗi ga mabuƙata, a turance ‘Cash Grant for Vulnerable Groups’ wanda aka yi a zauren majalisa na Gidan Gwamnati a Gusau.

  • Babu Abin Da Zai Kawo Min Cikas Wajen Inganta Rayuwar Jama’a – Sadiya Farou

Gwamna Matawalle ya lissafa alfanun da jihar sa ta samu daga Shirye-Shiryen Inganta Rayuwar Jama’ar Ƙasa (NSIPs), sannan ya yaba wa Ministar da Shugaba Muhammadu Buhari saboda ƙoƙarin su na rage fatara da yunwa a Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Ya ce: “Ministar ta na ta ƙoƙarin tabbatar da cewa ita nagartacciyar ‘ya ce daga jihar mu. Hakan a bayyane ya ke idan an yi la’akari da jerin shirye-shiryen Gwamnatin Tarayya na agajin jama’a wanda ma’aikatar ta ke aiwatarwa, waɗanda jihar mu ta amfana ƙwarai da gaske daga gare su.

“Haka kuma mun ga haka ta wajen ƙaunar da ta ke nuna wa wannan gwamnatin a kowane lokaci.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

“Na fahimci cewa ministar ta zo Jihar Zamfara ne domin ta rarraba kayan abinci da sauran kayayyaki ga ‘yan gudun hijira, kuma ta ƙaddamar da Shirin Ba Da Tallafin Kuɗi ga Mabuƙata, kuma ta raba takardun kama aiki ga ma’aikata ‘yan sa ido masu zaman kan su da aka ɗauka, sannan kuma ta ba da rance maras ruwa ga manoma da mata ‘yan kasuwa.

“Waɗannan abubuwan hoɓɓasa da ake yi wasu muhimman matakai ne da ake ɗauka domin a rage fatara tare da ƙarfafa wa mutanen mu gwiwa ta fuskar tattalin arziki. Halin ƙunci da ake ciki a ƙasar nan ya na buƙatar gwamnatoci a kowane mataki su dage su yi aiki wurjanjan. Wannan ƙoƙarin ya na zuwa ne a matsayin ɗori a kan ƙoƙarin da gwamnatin wannan jihar ke yi ta fuskoki da dama
domin ta sauƙaƙa wa jama’ar wannan jihar.”

A nata jawabin, Minista Sadiya Umar Farouq ta bayyana cewa ma’aikatar ta za ta raba agajin kuɗi ga mabuƙata 4,728 da ke Ƙananan Hukumomi 14 da ke faɗin jihar, yayin da an tantance tare da lissafa mutum 4,616 da za su ci moriyar lamunin Shirin Tallafin Kasuwanci na Gwamnati (wato GEEP) wanda babu ruwa a cikin sa, wanda ya kama daga N50,000 zuwa N300,000.

Ministar ta kuma ƙaddamar da Shirin Faɗakarwa na Ƙasa kan Shirin Ciyar Da Ɗalibai tare da ɗaukar ma’aikata ‘yan sa ido su 130, da sauran ayyuka.

A Jihar Zamfara dai, mutum 800 ne masu cin moriyar waɗanda su ka haɗa da naƙasassu da kuma tsofaffi waɗanda za a ba kyautar N50,000 kowannen su.

Daga bisani, ministar ta ziyarci ɗaya daga cikin sansanonin ‘yan gudun hijira inda ta raba kayan abinci da sauran kayan masarufi, ta kuma ƙaddamar da wani laburare tare da raba kayan cin abinci ga ‘yan makaranta a ƙarƙashin Shirin Ciyar Da ‘Yan Makaranta.

Farouq
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Farouq
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Farouq
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
An Nada Muhammad Bin Salman A Matsayin Sabon Firaministan Saudiyya

An Nada Muhammad Bin Salman A Matsayin Sabon Firaministan Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.