• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfarawa Na Alfahari Da Sadiya Umar Farouq – Gwamna Matawalle

by Sulaiman
3 years ago
in Rahotonni
0
Zamfarawa Na Alfahari Da Sadiya Umar Farouq – Gwamna Matawalle
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Bello Muhammed Matawalle na Jihar Zamfara ya bayyana Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, a matsayin nagatartacciyar ‘yar jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne kwanan nan a wajen ƙaddamar da shirin ba da tallafin kuɗi ga mabuƙata, a turance ‘Cash Grant for Vulnerable Groups’ wanda aka yi a zauren majalisa na Gidan Gwamnati a Gusau.

  • Babu Abin Da Zai Kawo Min Cikas Wajen Inganta Rayuwar Jama’a – Sadiya Farou

Gwamna Matawalle ya lissafa alfanun da jihar sa ta samu daga Shirye-Shiryen Inganta Rayuwar Jama’ar Ƙasa (NSIPs), sannan ya yaba wa Ministar da Shugaba Muhammadu Buhari saboda ƙoƙarin su na rage fatara da yunwa a Nijeriya.

Ya ce: “Ministar ta na ta ƙoƙarin tabbatar da cewa ita nagartacciyar ‘ya ce daga jihar mu. Hakan a bayyane ya ke idan an yi la’akari da jerin shirye-shiryen Gwamnatin Tarayya na agajin jama’a wanda ma’aikatar ta ke aiwatarwa, waɗanda jihar mu ta amfana ƙwarai da gaske daga gare su.

“Haka kuma mun ga haka ta wajen ƙaunar da ta ke nuna wa wannan gwamnatin a kowane lokaci.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

“Na fahimci cewa ministar ta zo Jihar Zamfara ne domin ta rarraba kayan abinci da sauran kayayyaki ga ‘yan gudun hijira, kuma ta ƙaddamar da Shirin Ba Da Tallafin Kuɗi ga Mabuƙata, kuma ta raba takardun kama aiki ga ma’aikata ‘yan sa ido masu zaman kan su da aka ɗauka, sannan kuma ta ba da rance maras ruwa ga manoma da mata ‘yan kasuwa.

“Waɗannan abubuwan hoɓɓasa da ake yi wasu muhimman matakai ne da ake ɗauka domin a rage fatara tare da ƙarfafa wa mutanen mu gwiwa ta fuskar tattalin arziki. Halin ƙunci da ake ciki a ƙasar nan ya na buƙatar gwamnatoci a kowane mataki su dage su yi aiki wurjanjan. Wannan ƙoƙarin ya na zuwa ne a matsayin ɗori a kan ƙoƙarin da gwamnatin wannan jihar ke yi ta fuskoki da dama
domin ta sauƙaƙa wa jama’ar wannan jihar.”

A nata jawabin, Minista Sadiya Umar Farouq ta bayyana cewa ma’aikatar ta za ta raba agajin kuɗi ga mabuƙata 4,728 da ke Ƙananan Hukumomi 14 da ke faɗin jihar, yayin da an tantance tare da lissafa mutum 4,616 da za su ci moriyar lamunin Shirin Tallafin Kasuwanci na Gwamnati (wato GEEP) wanda babu ruwa a cikin sa, wanda ya kama daga N50,000 zuwa N300,000.

Ministar ta kuma ƙaddamar da Shirin Faɗakarwa na Ƙasa kan Shirin Ciyar Da Ɗalibai tare da ɗaukar ma’aikata ‘yan sa ido su 130, da sauran ayyuka.

A Jihar Zamfara dai, mutum 800 ne masu cin moriyar waɗanda su ka haɗa da naƙasassu da kuma tsofaffi waɗanda za a ba kyautar N50,000 kowannen su.

Daga bisani, ministar ta ziyarci ɗaya daga cikin sansanonin ‘yan gudun hijira inda ta raba kayan abinci da sauran kayan masarufi, ta kuma ƙaddamar da wani laburare tare da raba kayan cin abinci ga ‘yan makaranta a ƙarƙashin Shirin Ciyar Da ‘Yan Makaranta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Haramta Siyan Makamai Ga Jami’an Tsaron Sa-Kai A Jihohi

Next Post

An Nada Muhammad Bin Salman A Matsayin Sabon Firaministan Saudiyya

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

3 weeks ago
Farouq
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

4 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

4 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 month ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 month ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
An Nada Muhammad Bin Salman A Matsayin Sabon Firaministan Saudiyya

An Nada Muhammad Bin Salman A Matsayin Sabon Firaministan Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.