• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Zaman Lafiya Ake Samun Ci Gaba – Sanata Uba Sani 

by Ibrahim Ibrahim
3 years ago
Sanata

Dan takarar gwaman jihar Kaduna a jam’iyyar APC Sanata Uba Sani, ya bayyana cewa, za a iya samar da ci gaba a cikin al’umma ne kawai idan akwai dawammamen zaman lafiya.

Sanata Uba Sani ya yi wannan bayani nea yayin ganawa da al’ummar Manchok, shalkwar karamar hukumar Kaura, inda ya yi alkawarin kirkiro da sana’o’in hannu, musamman ga mata da matasa don su zama masu dogaro da kan su ganin cewa gwamnati ba za ta iya daukar dubban matasan da ke a jihar ba aiki ba.

“Ilimin boko na da matukar mahimmanci wurin kara inganta rayuwar ko wacce irin al’umma tare da kuma habaka tattalin arzikin al’ummar.” In ji shi.

Dan takarar ya kara da cewa, akwai gibin da ake da shi na koyon sana’o’in hannu a jihar Kaduna wanda akwai matukar bukatar a cike shi.

Sanata

LABARAI MASU NASABA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

A cewar sa, Idan al’ummar jihar Kaduna su ka kada masa kuri’un su a shekarar 2023, gwamnatin sa za ta tabbatar da bayar da horo ga matasa a fannin koyon sana’o’in hannu domin su kasance sun tsaya da kafafun su, musamman domin a kara ciyar da tattalin arzikin jihar a gaba.

Sai dai kuma, Sanata Uba Sani ya ce, “Za a iya samun wannan nasarar ce, idan akwai dawammamen zaman lafiya. Ya zama wajibi mu mayar da hankulan mu wurinn ciyar da jihar da kuma Nijeriya gaba.

Sanata

Sanatan ya yi nuni da cewa, dole ne mu tabbatar da mun kau da dukkan banbance -banbance na kabila da na addini domin samun kai wa ga gaci.

Dan takarar kafin gudanar ganawar sa da gangamin yakin neman zaben sa a garin, ya kuma kai zirar ban girma ga Cif na Atakar.

Daga bisani, Sanata Uba Sani ya kuma ziyarci Kafanchan shalkwar karamar hukumar Jema’a, Kaura da Zangon Kataf, inda ya yi wa al’umma jawabi tare da yin kira a gare su da su zabi jam’iyyar APC tun daga kasa har sama a zaben shekarar 2023.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 
Manyan Labarai

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC
Manyan Labarai

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Next Post
Zan Fifita Bangaren Ilimi Idan Na Zama Gwamnan Jihar Kaduna- Sanata Uba Sani

Zan Fifita Bangaren Ilimi Idan Na Zama Gwamnan Jihar Kaduna- Sanata Uba Sani

LABARAI MASU NASABA

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.