ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Fifita Bangaren Ilimi Idan Na Zama Gwamnan Jihar Kaduna- Sanata Uba Sani

by Ibrahim Ibrahim
3 years ago
uba sani

Dan takarar zama gwamnan jihar Kaduna a jam’iyyar APC, Sanata Uba Sani, ya yi alkawarin ci gaba da ba harkar ilimi fifiko idan har aka zabe shi ya zama gwamna a zabe mai zuwa.

Uba Sani, ya ce, “Gwamnatin PDP ta yi watsi da makarantun gwamnati a cikin shekaru 16 da jam’iyyar ta yi tana mulki, ya yi alkawarin ci gaba daga inda gwamna Malam Nasir Ahmad El-Rufai ya tsaya, musamman bangaren inganta ilimi, idan ya samu damar zama gwamna.”

  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

 

ADVERTISEMENT

Sanatan ya bayyana haka ne a wurin taron kaddamar da yakin neman zaben sa a garin Giwa da ke jihar Kaduna a ranar Talata, 17 ga Janairu, 2023.

Dan takarar gwamnan wanda ya ce gwamna El-Rufai ya dawo da martabar da aka rasa a makarantun gwamnati, ya ce: “Abin da na sa a gaba shi ne na samar da ingantaccen ilimi ga ‘yan’uwa talakawa domin hakan ne zai ba su damar samun kyakkyawar makoma da kuma inganta al’umma gaba daya.”

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Haka kuma yi alkawarin karfafa malaman addini tun kafin zaben gwamna na 2023 a jihar, inda ya kara da cewa su na taka muhimmiyar rawa wurin gyara al’umma.

uba sani

Dan takarar gwamnan ya gode wa al’ummar karamar hukumar Giwa bisa goyon bayan gwamnatin APC a matakin tarayya, jiha da kananan hukumomi.

Ya kuma ce, “Ayyukan da aka aiwatar a cikin karamar hukumar Giwa ba za su yiwu ba idan ba tare da tallafin ku ba. Ina so ku ci-gaba da mara wa jamiiyar APC baya ta hanyar zaben jam’iyyar mu a dukkan matakai a zabe mai zuwa,” in ji shi.

Da ya ke jawabi a wurin gangamin, Gwamna Malam Nasir El-Rufai ya bukaci al’ummar Giwa da su zabi Sanata Uba Sani a matsayin magajin sa da kuma Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe a matsayin mataimakiyar sa saboda su na cikin tawagar su ka taimaka wurinn kawo sauyi a jihar Kaduna a karkashin jagoranci na.

Gwamnan ya kuma umarci jama’a da su zabi Muhammad Sani Abdullahi (Dattijo) a matsayin sanata mai wakiltar shiyya ta biyu da Honarabul Bashir Zubairu a matsayin dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Giwa da Birnin Gwari.

Ya kuma bukace su da su zabi ‘yan takarar mazabar Giwa ta Gabas da Yamma.

A yayin kamfen din, Mataimakiyar gwamnan ta kaddamar da cibiyar kula da mata masu juna biyu yayin da El-Rufai ya kaddamar da cibiyar wasanni na Unguwa gabanin taron.

Gwamna Nasir El-Rufa’i Sanata Uba Sani, mataimakiyar gwamna Hadiza Sabuwa Balarabe da sauran jami’an gwamnati sun kuma gana da masu ruwa da tsaki, inda suka gabatar da tambayoyi tare da bayyana wasu manufofin gwamnati.

uba sani
Ibrahim Ibrahim
+ postsBio
  • Ibrahim Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-ibrahim/
    Da Ɗumi-ɗuminsa: An Sa Dokar Hana Fita A Wasu Unguwannin Kaduna
  • Ibrahim Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-ibrahim/
    Kungiyar Ibo A Jihar Kaduna Ta Nuna Goyon Bayan Ga Sanata Uba Sani
  • Ibrahim Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-ibrahim/
    Da Zaman Lafiya Ake Samun Ci Gaba – Sanata Uba Sani 

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Ra’ayoyinku A Kan Wa’adin CBN Na Dakatar Da Karbar Tsofaffin Takardun Naira

Ra’ayoyinku A Kan Wa’adin CBN Na Dakatar Da Karbar Tsofaffin Takardun Naira

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.