ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Fifita Bangaren Ilimi Idan Na Zama Gwamnan Jihar Kaduna- Sanata Uba Sani

by Ibrahim Ibrahim
3 years ago
uba sani

Dan takarar zama gwamnan jihar Kaduna a jam’iyyar APC, Sanata Uba Sani, ya yi alkawarin ci gaba da ba harkar ilimi fifiko idan har aka zabe shi ya zama gwamna a zabe mai zuwa.

Uba Sani, ya ce, “Gwamnatin PDP ta yi watsi da makarantun gwamnati a cikin shekaru 16 da jam’iyyar ta yi tana mulki, ya yi alkawarin ci gaba daga inda gwamna Malam Nasir Ahmad El-Rufai ya tsaya, musamman bangaren inganta ilimi, idan ya samu damar zama gwamna.”

  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

 

ADVERTISEMENT

Sanatan ya bayyana haka ne a wurin taron kaddamar da yakin neman zaben sa a garin Giwa da ke jihar Kaduna a ranar Talata, 17 ga Janairu, 2023.

Dan takarar gwamnan wanda ya ce gwamna El-Rufai ya dawo da martabar da aka rasa a makarantun gwamnati, ya ce: “Abin da na sa a gaba shi ne na samar da ingantaccen ilimi ga ‘yan’uwa talakawa domin hakan ne zai ba su damar samun kyakkyawar makoma da kuma inganta al’umma gaba daya.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Haka kuma yi alkawarin karfafa malaman addini tun kafin zaben gwamna na 2023 a jihar, inda ya kara da cewa su na taka muhimmiyar rawa wurin gyara al’umma.

uba sani

Dan takarar gwamnan ya gode wa al’ummar karamar hukumar Giwa bisa goyon bayan gwamnatin APC a matakin tarayya, jiha da kananan hukumomi.

Ya kuma ce, “Ayyukan da aka aiwatar a cikin karamar hukumar Giwa ba za su yiwu ba idan ba tare da tallafin ku ba. Ina so ku ci-gaba da mara wa jamiiyar APC baya ta hanyar zaben jam’iyyar mu a dukkan matakai a zabe mai zuwa,” in ji shi.

Da ya ke jawabi a wurin gangamin, Gwamna Malam Nasir El-Rufai ya bukaci al’ummar Giwa da su zabi Sanata Uba Sani a matsayin magajin sa da kuma Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe a matsayin mataimakiyar sa saboda su na cikin tawagar su ka taimaka wurinn kawo sauyi a jihar Kaduna a karkashin jagoranci na.

Gwamnan ya kuma umarci jama’a da su zabi Muhammad Sani Abdullahi (Dattijo) a matsayin sanata mai wakiltar shiyya ta biyu da Honarabul Bashir Zubairu a matsayin dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Giwa da Birnin Gwari.

Ya kuma bukace su da su zabi ‘yan takarar mazabar Giwa ta Gabas da Yamma.

A yayin kamfen din, Mataimakiyar gwamnan ta kaddamar da cibiyar kula da mata masu juna biyu yayin da El-Rufai ya kaddamar da cibiyar wasanni na Unguwa gabanin taron.

Gwamna Nasir El-Rufa’i Sanata Uba Sani, mataimakiyar gwamna Hadiza Sabuwa Balarabe da sauran jami’an gwamnati sun kuma gana da masu ruwa da tsaki, inda suka gabatar da tambayoyi tare da bayyana wasu manufofin gwamnati.

uba sani
Ibrahim Ibrahim
+ postsBio
  • Ibrahim Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-ibrahim/
    Da Ɗumi-ɗuminsa: An Sa Dokar Hana Fita A Wasu Unguwannin Kaduna
  • Ibrahim Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-ibrahim/
    Kungiyar Ibo A Jihar Kaduna Ta Nuna Goyon Bayan Ga Sanata Uba Sani
  • Ibrahim Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-ibrahim/
    Da Zaman Lafiya Ake Samun Ci Gaba – Sanata Uba Sani 

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Next Post
Ra’ayoyinku A Kan Wa’adin CBN Na Dakatar Da Karbar Tsofaffin Takardun Naira

Ra’ayoyinku A Kan Wa’adin CBN Na Dakatar Da Karbar Tsofaffin Takardun Naira

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.