• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Kin Gaskiya Sai Bata

by Sulaiman and CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Daga Kin Gaskiya Sai Bata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

Yayin da yanayin tattalin arzikin kasashen duniya ke kara fuskantar halin rashin tabbas, kana kasashe da dama na cigaba da fafutukar yadda zasu cike komadar tattalin arzikin dake addabarsu, a hannu guda kuma, wasu daga cikin manyan kasashe masu karfin fada aji ta fuskar tattalin arzikin su ma suna dandana irin tasu kudar.

Koda yake, wasu kasashen suna girbar abinda suka shuka ne a samakon daukar wasu matakai na bisa son zuciyarsu, ko kuma sun dauki matakan a bisa kuskure, ba tare da sun yi dogon tunani mai zurfi gabanin daukar irin wadannan matakai ko kuma yanke irin wannan danyen hukunci ba, wanda galibin wadannan matakai nadama ce ke biyo bayan yankesu, sannan lamarin yayi matukar haifar da mummunan tasiri tare da jefa alummunsu cikin halin ha’ula’i.

Alal misali, a karshen wannan mako, wasu masanan kasar Amurka da dama suna ci gaba da yin kira ga gwamnatin shugaban kasar Amurka Joe Biden, da ta soke harajin da aka sanya a lokacin gwamnatin Trump kan kayayyakin da ake shigo da su daga kasar Sin, inda suka jaddada cewa, kawo karshen yakin ciniki a tsakanin kasashen Sin da Amurka zai yi matukar amfanawa Amurkawa. Anton Bekkerman, wani masanin tattalin arzki a fannin aikin gona ne, kana darakta cibiyar nazarin aikin noma ta jahar New Hampshire ya ce, “lokaci ya yi da ya kamata a fara tunanin yadda za a ci gaba, maimakon kirkiro wani abin da zai mayar da hannun agogo baya,” a cewar masanin, wanda kuma shi ne mataimakin shugaban sashen nazarin kimiyyar rayuwa da aikin gona a jami’ar New Hampshire ta Amurka.

Ya ce, kara kudaden harajin kwastan ba manufofi ne masu alfanu ba, kamar yadda ya bayyana a zantawarsa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a baya-bayan nan. Shi ma Vincent Smith, masanin tattalin arziki, kuma shehun malamin jami’ar Montana, ya bayyana a kwanan nan cewa, “Za a iya bayyana takaddamar kasuwancin a matsayin wani babban koma bayan tattalin arziki da gwamnatin Trump ta aiwatar, saboda abin takaici ne da rashin tunani game da hakikanin yadda duniya ke gudana, wanda wasu daga cikin mashawartan tsohon shugaban suka dinga ingiza jagoran kasar na wancan lokaci.” Tun a farkon wannan shekara, wasu alkaluman da sashen ayyukan gona na Amurka ya fitar sun nuna cewa, yakin cinikin da gwamnatin Trump ta assasa, ya jawowa fannin aikin gonar Amurka hasarar dalar Amurka kusan biliyan 27 a cikin shekaru biyun da suka gabata. Ko shakka babu, wannan al’amarin ya haifar da mummunan tasiri ga tattalin arzikin Washingtom, kuma abu mafi muhimmanci shine, ya kamata gwamnatin Biden ta sake tunani, domin ance, “ita gaskiya bata bukatar ado,” kuma “daga kin gaskiya sai bata.” (Ahmad)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Sanda Sun Cafke Dan Sandan Bogi A Ebonyi

Next Post

Saudiyya Ta Kara Wa Maniyyatan Nijeriya Kwanakin Jigilar Alhazai

Related

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi
Daga Birnin Sin

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

2 hours ago
Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

3 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

4 hours ago
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

5 hours ago
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

24 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

1 day ago
Next Post
Saudiyya Ta Kara Wa Maniyyatan Nijeriya Kwanakin Jigilar Alhazai

Saudiyya Ta Kara Wa Maniyyatan Nijeriya Kwanakin Jigilar Alhazai

LABARAI MASU NASABA

Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

August 27, 2025
Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

August 27, 2025
Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

August 27, 2025
Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

August 27, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

August 27, 2025
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

August 27, 2025
Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

August 27, 2025
Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.