• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Kin Gaskiya Sai Bata

by Sulaiman and CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Daga Kin Gaskiya Sai Bata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

Kayan Aro Baya Rufe Katara

Yayin da yanayin tattalin arzikin kasashen duniya ke kara fuskantar halin rashin tabbas, kana kasashe da dama na cigaba da fafutukar yadda zasu cike komadar tattalin arzikin dake addabarsu, a hannu guda kuma, wasu daga cikin manyan kasashe masu karfin fada aji ta fuskar tattalin arzikin su ma suna dandana irin tasu kudar.

Koda yake, wasu kasashen suna girbar abinda suka shuka ne a samakon daukar wasu matakai na bisa son zuciyarsu, ko kuma sun dauki matakan a bisa kuskure, ba tare da sun yi dogon tunani mai zurfi gabanin daukar irin wadannan matakai ko kuma yanke irin wannan danyen hukunci ba, wanda galibin wadannan matakai nadama ce ke biyo bayan yankesu, sannan lamarin yayi matukar haifar da mummunan tasiri tare da jefa alummunsu cikin halin ha’ula’i.

Alal misali, a karshen wannan mako, wasu masanan kasar Amurka da dama suna ci gaba da yin kira ga gwamnatin shugaban kasar Amurka Joe Biden, da ta soke harajin da aka sanya a lokacin gwamnatin Trump kan kayayyakin da ake shigo da su daga kasar Sin, inda suka jaddada cewa, kawo karshen yakin ciniki a tsakanin kasashen Sin da Amurka zai yi matukar amfanawa Amurkawa. Anton Bekkerman, wani masanin tattalin arzki a fannin aikin gona ne, kana darakta cibiyar nazarin aikin noma ta jahar New Hampshire ya ce, “lokaci ya yi da ya kamata a fara tunanin yadda za a ci gaba, maimakon kirkiro wani abin da zai mayar da hannun agogo baya,” a cewar masanin, wanda kuma shi ne mataimakin shugaban sashen nazarin kimiyyar rayuwa da aikin gona a jami’ar New Hampshire ta Amurka.

Ya ce, kara kudaden harajin kwastan ba manufofi ne masu alfanu ba, kamar yadda ya bayyana a zantawarsa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a baya-bayan nan. Shi ma Vincent Smith, masanin tattalin arziki, kuma shehun malamin jami’ar Montana, ya bayyana a kwanan nan cewa, “Za a iya bayyana takaddamar kasuwancin a matsayin wani babban koma bayan tattalin arziki da gwamnatin Trump ta aiwatar, saboda abin takaici ne da rashin tunani game da hakikanin yadda duniya ke gudana, wanda wasu daga cikin mashawartan tsohon shugaban suka dinga ingiza jagoran kasar na wancan lokaci.” Tun a farkon wannan shekara, wasu alkaluman da sashen ayyukan gona na Amurka ya fitar sun nuna cewa, yakin cinikin da gwamnatin Trump ta assasa, ya jawowa fannin aikin gonar Amurka hasarar dalar Amurka kusan biliyan 27 a cikin shekaru biyun da suka gabata. Ko shakka babu, wannan al’amarin ya haifar da mummunan tasiri ga tattalin arzikin Washingtom, kuma abu mafi muhimmanci shine, ya kamata gwamnatin Biden ta sake tunani, domin ance, “ita gaskiya bata bukatar ado,” kuma “daga kin gaskiya sai bata.” (Ahmad)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Sanda Sun Cafke Dan Sandan Bogi A Ebonyi

Next Post

Saudiyya Ta Kara Wa Maniyyatan Nijeriya Kwanakin Jigilar Alhazai

Related

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

4 hours ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Daga Birnin Sin

Kayan Aro Baya Rufe Katara

5 hours ago
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

6 hours ago
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 
Daga Birnin Sin

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

7 hours ago
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

8 hours ago
Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa

9 hours ago
Next Post
Saudiyya Ta Kara Wa Maniyyatan Nijeriya Kwanakin Jigilar Alhazai

Saudiyya Ta Kara Wa Maniyyatan Nijeriya Kwanakin Jigilar Alhazai

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.