• English
  • Business News
Monday, June 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Munich Zuwa Addis Ababa, Ci Gaban Kasashe Daban Daban Na Tabbata

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Daga Munich Zuwa Addis Ababa, Ci Gaban Kasashe Daban Daban Na Tabbata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Duniya na sauya salonta. Me ya kamata mu yi don fuskantar duniyar da kasashe daban daban ke tabbatar da ci gabansu na bai daya?” An gudanar da taron shekara shekara kan harkokin tsaro a birnin Munich na kasar Jamus a kwanan baya, kuma faifan bidiyo na tallata taron ya mika wannan tambaya ga mahalarta taron. Kafin budewar taron kuma, masu shirya taron sun gabatar da rahoton tsaro na Munich na shekarar 2025 wanda ke da taken “bunkasar kasashe daban daban na bai daya”, wanda yake ganin cewa, “bunkasar kasashe daban daban na bai daya ya zama tabbas.” 

Kusan a lokaci guda ne, aka gudanar da taron kolin kungiyar tarayyar Afirka a birnin Addis Ababa, taron da aka sanya wa taken “tabbatar da adalci ga ‘yan Afirka da zuriyoyinsu ta hanyar biyan diyya”. Kasancewarta nahiyar da aka fi samun kasashe masu tasowa a duniya, yadda kasashen nahiyar suka fito da muryarsu ta tsayawa kan kafafuwansu da ma gyara kura-kurai na rashin adalci a gare su, shi ma ya shaida mana karatowar zamanin da kasashe daban daban ke tabbatar da bunkasarsu ta bai daya.

  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 2 Da Ake Zargi Da Yi Wa Yarinya ‘Yar Shekara 12 Fyade A Yobe
  • Ƴan Ta’adda Sun Sako Manoma 11, Sun Rike 3 A Borno

A cikin shekaru daruruwa da suka gabata, kasashen yammacin duniya sun bunkasa bisa ga tarin dukuyoyin da suka kwace daga kasashen Afirka, lamarin da ya sa har yanzu al’ummar kasashen Afirka ke fuskantar talauci. Sai dai ba a kai ga gyara wannan yanayi na rashin adalci da ake ciki a karkashin tsarin duniya da kasashen yamma ke jagoranta ba. A wannan karon, kungiyar tarayyar Afirka ta gabatar da bukatar gyara kura-kuran, kuma hakan ya faru ne daidai saboda yanayin da suka samu kansu a ciki na bunkasar kasashe daban daban, musamman ma yadda kasashe masu tasowa suka kara karfinsu har suka fara taka muhimmiyar rawa a duniya.

A hakika, ba kudade kawai kasashen Afirka suke bukatar a biya su ba, suna kuma neman wargaza irin tsarin tattalin arzikin da suke dogara ga kasashen da a baya suka yi musu mulkin mallaka, wato irin tsarin wawushe albarkatunsu da aka kafa a lokacin mulkin mallaka har yanzu suna aiki. Alkaluman da MDD ta samar sun shaida cewa, nahiyar Afirka na da kaso 30% na ma’adinan duniya, sai dai yawan cinikin da kasashen Afirka suke yi bai kai kaso 3% na duniya ba, kuma kayayyakin da suke samarwa ya kai kaso 1.9% na duniya ne kawai. Daidai kamar yadda Mr. Claver Gatete, sakataren zartaswa na kwamitin kula da tattalin arzikin Afirka na MDD ya fada, abin da ake nufi da biyan diyya shi ne, ya zama dole albarkatun Afirka su amfana wa Afirka, kuma a kafa masana’antu a kasashen Afirka, a fadada tsarin masana’antu a kasashen.

A yayin da yake halartar taron tsaro na Munich na wannan shekara, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi nuni da cewa, ya kamata a wanzar da adalci da oda a yanayin da duniya ke ciki na samun bunkasar kasashe daban daban. Ya jaddada cewa, kiyaye adalci ta fannonin ikon kasa da kasa da damammakinsu da ma ka’idojin da suke bi, ya kamata ya zama tushen gina duniya da kasashe daban daban ke tabbatar da bunkasarsu ta bai daya. A hakika, kasancewarta babbar kasa mai tasowa wanda ke goyon bayan bunkasar kasashen duniya na bai daya, har kullum kasar Sin na neman kyautata wakilcin kasashe masu tasowa, musamman na kasashe Afirka, a tsarin duniya, tana kuma kokarin more damammakinta ga kasa da kasa, don tallafawa bunkasuwar kasashen duniya na bai daya. A game da hakan, tsohon ministan harkokin wajen tarayyar Nijeriya, Ibrahim Gambari ya ce, kasar Sin ita ce ta farko a duniya da ta bayyana a fili goyon bayanta ga shigar kungiyar tarayyar Afirka G20, matakin da ya shaida yadda kasar Sin ke goyon bayan kasashen Afirka wajen kara fitowa da muryarsu a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

Bunkasar kasashen duniya na bai daya ya zama tabbas, wanda kuma yake tabbata. Kamar yadda shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama ya bayyana a wajen taron tsaro na Munich, “Kasashe daban daban na tabbatar da bunkasarsu yanzu a maimakon yadda muke a baya. A lokacin da aka kone tsoffin gadoji, ana gina sabbi…kuma ya kamata mu sake hada kasashen duniya bisa wadannan sabbin gadoji.” (Lubabatu)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kebbi Ta Samar Da Tirela 300 Na Abinci Don Rabo Da Azumi

Next Post

Tsaro: NSA Ya Miƙa Wa Gwamnatin Kaduna Mutane 59 Da Aka Kuɓutar 

Related

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

1 day ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

3 days ago
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

6 days ago
Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a
Ra'ayi Riga

Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a

2 weeks ago
Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

2 weeks ago
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya
Ra'ayi Riga

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

2 weeks ago
Next Post
Tsaro: NSA Ya Miƙa Wa Gwamnatin Kaduna Mutane 59 Da Aka Kuɓutar 

Tsaro: NSA Ya Miƙa Wa Gwamnatin Kaduna Mutane 59 Da Aka Kuɓutar 

LABARAI MASU NASABA

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

June 8, 2025
Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

June 8, 2025
Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

June 8, 2025
Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

June 8, 2025
Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

June 8, 2025
Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

June 8, 2025
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

June 8, 2025
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.