ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Munich Zuwa Addis Ababa, Ci Gaban Kasashe Daban Daban Na Tabbata

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Addis Ababa

“Duniya na sauya salonta. Me ya kamata mu yi don fuskantar duniyar da kasashe daban daban ke tabbatar da ci gabansu na bai daya?” An gudanar da taron shekara shekara kan harkokin tsaro a birnin Munich na kasar Jamus a kwanan baya, kuma faifan bidiyo na tallata taron ya mika wannan tambaya ga mahalarta taron. Kafin budewar taron kuma, masu shirya taron sun gabatar da rahoton tsaro na Munich na shekarar 2025 wanda ke da taken “bunkasar kasashe daban daban na bai daya”, wanda yake ganin cewa, “bunkasar kasashe daban daban na bai daya ya zama tabbas.” 

Kusan a lokaci guda ne, aka gudanar da taron kolin kungiyar tarayyar Afirka a birnin Addis Ababa, taron da aka sanya wa taken “tabbatar da adalci ga ‘yan Afirka da zuriyoyinsu ta hanyar biyan diyya”. Kasancewarta nahiyar da aka fi samun kasashe masu tasowa a duniya, yadda kasashen nahiyar suka fito da muryarsu ta tsayawa kan kafafuwansu da ma gyara kura-kurai na rashin adalci a gare su, shi ma ya shaida mana karatowar zamanin da kasashe daban daban ke tabbatar da bunkasarsu ta bai daya.

  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 2 Da Ake Zargi Da Yi Wa Yarinya ‘Yar Shekara 12 Fyade A Yobe
  • Ƴan Ta’adda Sun Sako Manoma 11, Sun Rike 3 A Borno

A cikin shekaru daruruwa da suka gabata, kasashen yammacin duniya sun bunkasa bisa ga tarin dukuyoyin da suka kwace daga kasashen Afirka, lamarin da ya sa har yanzu al’ummar kasashen Afirka ke fuskantar talauci. Sai dai ba a kai ga gyara wannan yanayi na rashin adalci da ake ciki a karkashin tsarin duniya da kasashen yamma ke jagoranta ba. A wannan karon, kungiyar tarayyar Afirka ta gabatar da bukatar gyara kura-kuran, kuma hakan ya faru ne daidai saboda yanayin da suka samu kansu a ciki na bunkasar kasashe daban daban, musamman ma yadda kasashe masu tasowa suka kara karfinsu har suka fara taka muhimmiyar rawa a duniya.

ADVERTISEMENT

A hakika, ba kudade kawai kasashen Afirka suke bukatar a biya su ba, suna kuma neman wargaza irin tsarin tattalin arzikin da suke dogara ga kasashen da a baya suka yi musu mulkin mallaka, wato irin tsarin wawushe albarkatunsu da aka kafa a lokacin mulkin mallaka har yanzu suna aiki. Alkaluman da MDD ta samar sun shaida cewa, nahiyar Afirka na da kaso 30% na ma’adinan duniya, sai dai yawan cinikin da kasashen Afirka suke yi bai kai kaso 3% na duniya ba, kuma kayayyakin da suke samarwa ya kai kaso 1.9% na duniya ne kawai. Daidai kamar yadda Mr. Claver Gatete, sakataren zartaswa na kwamitin kula da tattalin arzikin Afirka na MDD ya fada, abin da ake nufi da biyan diyya shi ne, ya zama dole albarkatun Afirka su amfana wa Afirka, kuma a kafa masana’antu a kasashen Afirka, a fadada tsarin masana’antu a kasashen.

A yayin da yake halartar taron tsaro na Munich na wannan shekara, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi nuni da cewa, ya kamata a wanzar da adalci da oda a yanayin da duniya ke ciki na samun bunkasar kasashe daban daban. Ya jaddada cewa, kiyaye adalci ta fannonin ikon kasa da kasa da damammakinsu da ma ka’idojin da suke bi, ya kamata ya zama tushen gina duniya da kasashe daban daban ke tabbatar da bunkasarsu ta bai daya. A hakika, kasancewarta babbar kasa mai tasowa wanda ke goyon bayan bunkasar kasashen duniya na bai daya, har kullum kasar Sin na neman kyautata wakilcin kasashe masu tasowa, musamman na kasashe Afirka, a tsarin duniya, tana kuma kokarin more damammakinta ga kasa da kasa, don tallafawa bunkasuwar kasashen duniya na bai daya. A game da hakan, tsohon ministan harkokin wajen tarayyar Nijeriya, Ibrahim Gambari ya ce, kasar Sin ita ce ta farko a duniya da ta bayyana a fili goyon bayanta ga shigar kungiyar tarayyar Afirka G20, matakin da ya shaida yadda kasar Sin ke goyon bayan kasashen Afirka wajen kara fitowa da muryarsu a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Bunkasar kasashen duniya na bai daya ya zama tabbas, wanda kuma yake tabbata. Kamar yadda shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama ya bayyana a wajen taron tsaro na Munich, “Kasashe daban daban na tabbatar da bunkasarsu yanzu a maimakon yadda muke a baya. A lokacin da aka kone tsoffin gadoji, ana gina sabbi…kuma ya kamata mu sake hada kasashen duniya bisa wadannan sabbin gadoji.” (Lubabatu)

 

Addis Ababa
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Addis Ababa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Tsaro: NSA Ya Miƙa Wa Gwamnatin Kaduna Mutane 59 Da Aka Kuɓutar 

Tsaro: NSA Ya Miƙa Wa Gwamnatin Kaduna Mutane 59 Da Aka Kuɓutar 

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.