• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Munich Zuwa Addis Ababa, Ci Gaban Kasashe Daban Daban Na Tabbata

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Daga Munich Zuwa Addis Ababa, Ci Gaban Kasashe Daban Daban Na Tabbata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Duniya na sauya salonta. Me ya kamata mu yi don fuskantar duniyar da kasashe daban daban ke tabbatar da ci gabansu na bai daya?” An gudanar da taron shekara shekara kan harkokin tsaro a birnin Munich na kasar Jamus a kwanan baya, kuma faifan bidiyo na tallata taron ya mika wannan tambaya ga mahalarta taron. Kafin budewar taron kuma, masu shirya taron sun gabatar da rahoton tsaro na Munich na shekarar 2025 wanda ke da taken “bunkasar kasashe daban daban na bai daya”, wanda yake ganin cewa, “bunkasar kasashe daban daban na bai daya ya zama tabbas.” 

Kusan a lokaci guda ne, aka gudanar da taron kolin kungiyar tarayyar Afirka a birnin Addis Ababa, taron da aka sanya wa taken “tabbatar da adalci ga ‘yan Afirka da zuriyoyinsu ta hanyar biyan diyya”. Kasancewarta nahiyar da aka fi samun kasashe masu tasowa a duniya, yadda kasashen nahiyar suka fito da muryarsu ta tsayawa kan kafafuwansu da ma gyara kura-kurai na rashin adalci a gare su, shi ma ya shaida mana karatowar zamanin da kasashe daban daban ke tabbatar da bunkasarsu ta bai daya.

  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 2 Da Ake Zargi Da Yi Wa Yarinya ‘Yar Shekara 12 Fyade A Yobe
  • Ƴan Ta’adda Sun Sako Manoma 11, Sun Rike 3 A Borno

A cikin shekaru daruruwa da suka gabata, kasashen yammacin duniya sun bunkasa bisa ga tarin dukuyoyin da suka kwace daga kasashen Afirka, lamarin da ya sa har yanzu al’ummar kasashen Afirka ke fuskantar talauci. Sai dai ba a kai ga gyara wannan yanayi na rashin adalci da ake ciki a karkashin tsarin duniya da kasashen yamma ke jagoranta ba. A wannan karon, kungiyar tarayyar Afirka ta gabatar da bukatar gyara kura-kuran, kuma hakan ya faru ne daidai saboda yanayin da suka samu kansu a ciki na bunkasar kasashe daban daban, musamman ma yadda kasashe masu tasowa suka kara karfinsu har suka fara taka muhimmiyar rawa a duniya.

A hakika, ba kudade kawai kasashen Afirka suke bukatar a biya su ba, suna kuma neman wargaza irin tsarin tattalin arzikin da suke dogara ga kasashen da a baya suka yi musu mulkin mallaka, wato irin tsarin wawushe albarkatunsu da aka kafa a lokacin mulkin mallaka har yanzu suna aiki. Alkaluman da MDD ta samar sun shaida cewa, nahiyar Afirka na da kaso 30% na ma’adinan duniya, sai dai yawan cinikin da kasashen Afirka suke yi bai kai kaso 3% na duniya ba, kuma kayayyakin da suke samarwa ya kai kaso 1.9% na duniya ne kawai. Daidai kamar yadda Mr. Claver Gatete, sakataren zartaswa na kwamitin kula da tattalin arzikin Afirka na MDD ya fada, abin da ake nufi da biyan diyya shi ne, ya zama dole albarkatun Afirka su amfana wa Afirka, kuma a kafa masana’antu a kasashen Afirka, a fadada tsarin masana’antu a kasashen.

A yayin da yake halartar taron tsaro na Munich na wannan shekara, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi nuni da cewa, ya kamata a wanzar da adalci da oda a yanayin da duniya ke ciki na samun bunkasar kasashe daban daban. Ya jaddada cewa, kiyaye adalci ta fannonin ikon kasa da kasa da damammakinsu da ma ka’idojin da suke bi, ya kamata ya zama tushen gina duniya da kasashe daban daban ke tabbatar da bunkasarsu ta bai daya. A hakika, kasancewarta babbar kasa mai tasowa wanda ke goyon bayan bunkasar kasashen duniya na bai daya, har kullum kasar Sin na neman kyautata wakilcin kasashe masu tasowa, musamman na kasashe Afirka, a tsarin duniya, tana kuma kokarin more damammakinta ga kasa da kasa, don tallafawa bunkasuwar kasashen duniya na bai daya. A game da hakan, tsohon ministan harkokin wajen tarayyar Nijeriya, Ibrahim Gambari ya ce, kasar Sin ita ce ta farko a duniya da ta bayyana a fili goyon bayanta ga shigar kungiyar tarayyar Afirka G20, matakin da ya shaida yadda kasar Sin ke goyon bayan kasashen Afirka wajen kara fitowa da muryarsu a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

Bunkasar kasashen duniya na bai daya ya zama tabbas, wanda kuma yake tabbata. Kamar yadda shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama ya bayyana a wajen taron tsaro na Munich, “Kasashe daban daban na tabbatar da bunkasarsu yanzu a maimakon yadda muke a baya. A lokacin da aka kone tsoffin gadoji, ana gina sabbi…kuma ya kamata mu sake hada kasashen duniya bisa wadannan sabbin gadoji.” (Lubabatu)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kebbi Ta Samar Da Tirela 300 Na Abinci Don Rabo Da Azumi

Next Post

Tsaro: NSA Ya Miƙa Wa Gwamnatin Kaduna Mutane 59 Da Aka Kuɓutar 

Related

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

4 days ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

5 days ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

6 days ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

2 weeks ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

2 weeks ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

3 weeks ago
Next Post
Tsaro: NSA Ya Miƙa Wa Gwamnatin Kaduna Mutane 59 Da Aka Kuɓutar 

Tsaro: NSA Ya Miƙa Wa Gwamnatin Kaduna Mutane 59 Da Aka Kuɓutar 

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

July 8, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.