ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Munich Zuwa Addis Ababa, Ci Gaban Kasashe Daban Daban Na Tabbata

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Addis Ababa

“Duniya na sauya salonta. Me ya kamata mu yi don fuskantar duniyar da kasashe daban daban ke tabbatar da ci gabansu na bai daya?” An gudanar da taron shekara shekara kan harkokin tsaro a birnin Munich na kasar Jamus a kwanan baya, kuma faifan bidiyo na tallata taron ya mika wannan tambaya ga mahalarta taron. Kafin budewar taron kuma, masu shirya taron sun gabatar da rahoton tsaro na Munich na shekarar 2025 wanda ke da taken “bunkasar kasashe daban daban na bai daya”, wanda yake ganin cewa, “bunkasar kasashe daban daban na bai daya ya zama tabbas.” 

Kusan a lokaci guda ne, aka gudanar da taron kolin kungiyar tarayyar Afirka a birnin Addis Ababa, taron da aka sanya wa taken “tabbatar da adalci ga ‘yan Afirka da zuriyoyinsu ta hanyar biyan diyya”. Kasancewarta nahiyar da aka fi samun kasashe masu tasowa a duniya, yadda kasashen nahiyar suka fito da muryarsu ta tsayawa kan kafafuwansu da ma gyara kura-kurai na rashin adalci a gare su, shi ma ya shaida mana karatowar zamanin da kasashe daban daban ke tabbatar da bunkasarsu ta bai daya.

  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 2 Da Ake Zargi Da Yi Wa Yarinya ‘Yar Shekara 12 Fyade A Yobe
  • Ƴan Ta’adda Sun Sako Manoma 11, Sun Rike 3 A Borno

A cikin shekaru daruruwa da suka gabata, kasashen yammacin duniya sun bunkasa bisa ga tarin dukuyoyin da suka kwace daga kasashen Afirka, lamarin da ya sa har yanzu al’ummar kasashen Afirka ke fuskantar talauci. Sai dai ba a kai ga gyara wannan yanayi na rashin adalci da ake ciki a karkashin tsarin duniya da kasashen yamma ke jagoranta ba. A wannan karon, kungiyar tarayyar Afirka ta gabatar da bukatar gyara kura-kuran, kuma hakan ya faru ne daidai saboda yanayin da suka samu kansu a ciki na bunkasar kasashe daban daban, musamman ma yadda kasashe masu tasowa suka kara karfinsu har suka fara taka muhimmiyar rawa a duniya.

ADVERTISEMENT

A hakika, ba kudade kawai kasashen Afirka suke bukatar a biya su ba, suna kuma neman wargaza irin tsarin tattalin arzikin da suke dogara ga kasashen da a baya suka yi musu mulkin mallaka, wato irin tsarin wawushe albarkatunsu da aka kafa a lokacin mulkin mallaka har yanzu suna aiki. Alkaluman da MDD ta samar sun shaida cewa, nahiyar Afirka na da kaso 30% na ma’adinan duniya, sai dai yawan cinikin da kasashen Afirka suke yi bai kai kaso 3% na duniya ba, kuma kayayyakin da suke samarwa ya kai kaso 1.9% na duniya ne kawai. Daidai kamar yadda Mr. Claver Gatete, sakataren zartaswa na kwamitin kula da tattalin arzikin Afirka na MDD ya fada, abin da ake nufi da biyan diyya shi ne, ya zama dole albarkatun Afirka su amfana wa Afirka, kuma a kafa masana’antu a kasashen Afirka, a fadada tsarin masana’antu a kasashen.

A yayin da yake halartar taron tsaro na Munich na wannan shekara, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi nuni da cewa, ya kamata a wanzar da adalci da oda a yanayin da duniya ke ciki na samun bunkasar kasashe daban daban. Ya jaddada cewa, kiyaye adalci ta fannonin ikon kasa da kasa da damammakinsu da ma ka’idojin da suke bi, ya kamata ya zama tushen gina duniya da kasashe daban daban ke tabbatar da bunkasarsu ta bai daya. A hakika, kasancewarta babbar kasa mai tasowa wanda ke goyon bayan bunkasar kasashen duniya na bai daya, har kullum kasar Sin na neman kyautata wakilcin kasashe masu tasowa, musamman na kasashe Afirka, a tsarin duniya, tana kuma kokarin more damammakinta ga kasa da kasa, don tallafawa bunkasuwar kasashen duniya na bai daya. A game da hakan, tsohon ministan harkokin wajen tarayyar Nijeriya, Ibrahim Gambari ya ce, kasar Sin ita ce ta farko a duniya da ta bayyana a fili goyon bayanta ga shigar kungiyar tarayyar Afirka G20, matakin da ya shaida yadda kasar Sin ke goyon bayan kasashen Afirka wajen kara fitowa da muryarsu a duniya.

LABARAI MASU NASABA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Bunkasar kasashen duniya na bai daya ya zama tabbas, wanda kuma yake tabbata. Kamar yadda shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama ya bayyana a wajen taron tsaro na Munich, “Kasashe daban daban na tabbatar da bunkasarsu yanzu a maimakon yadda muke a baya. A lokacin da aka kone tsoffin gadoji, ana gina sabbi…kuma ya kamata mu sake hada kasashen duniya bisa wadannan sabbin gadoji.” (Lubabatu)

 

Addis Ababa
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Addis Ababa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
Tsaro: NSA Ya Miƙa Wa Gwamnatin Kaduna Mutane 59 Da Aka Kuɓutar 

Tsaro: NSA Ya Miƙa Wa Gwamnatin Kaduna Mutane 59 Da Aka Kuɓutar 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.