• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Yanzu Saudiyya Ce Za Ta Kula Da Abincin Alhazan Nijeriya -NAHCON

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
1 year ago
nahcon

Hukumar Kula Da Jin Dadin Alhazai ta Nijeriya (NAHCON) ta ce, hukumomi a kasar Saudi Arabiyya za su amshi ragamar kula da ciyar da maniyyata da samar musu da masauki a Makka da Madina, lamarin da zai fara kasancewa daga aikin hajjin 2025.

A wata sanarwar da kakakin NAHCON, Fatima Usara, ta fitar a makon jiya, ta ce, an cimma wannan fahimtar juna ne a wani tattaunawa ta yanar gizo da aka gudanar a tsakanin hukumar da ma’aikatar kula da aikin hajji da Umrah (MoHU) ta kasar Saudiyya.

  • Kaso 40 Na ‘Yan Nijeriya Na Samun Wutar Lantarki Fiye Da Awa 20 A Kowace Rana — Minista
  • APC Ta Lalata Nijeriya, PDP Kuma Matacciyar Jam’iyya Ce — Kwankwaso

Fatima ta kuma kara da cewa hukumar ta gudanar da ganawar fara shirye-shiryen gudanar da aikin hajjin da ke tafe da manyan sakatarorin kula da jin dadin alhazai na jihohi, wanda kwamishina a NAHCON, Anofi Elegushi ya jagoranta a ranar 23 ga watan Satumba.

A cewarta, Elegushi ya ce kamfanonin da hukumar alhazan Saudiyya ta assasa da aka fi sani da ‘mu’assasa’, su ne za su kula da ciyar da alhazai da samar musu da masauki a Makkah da Madina da zai fara daga 2025 bisa kulawar ma’aikatar MoHU.

“Wannan tsarin zai shafi dukkanin kasashen da za su halarci aikin hajji, kuma zai fara ne daga aikin hajjin 2025,” ya shaida.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Elegushi ya jaddada aniyar NAHCON na fara gudanar da shirye-shiryen aikin hajji bisa lokacin da Saudiyya ta bayar, kuma ya yi kira ga dukkanin masu ruwa da tsaki kan aikin hajji da su bayar da hadin kai.

Shugaban kungiyar jagororin hukumomin jin dadin alhazai na jihohi, Idris Almakura ya yaba wa NAHCON kan kokarinta da take kan yi, ya roki hukumar da ta ci gaba da daukan kyawawan tsare-tsaren da take bi.

Almakura ya nuna damuwarsa kan tsarin ajiyan kudin kujera, tsarin tawagar jami’an kiwon lafiya da kuma tsarin jinkirin maida wa maniyyata kudadensu.

Da yake maida jawabi, Elegushi ya yaba wa jagororin kula da aikin hajji na jihohi kan yunkurinsu na sanar da tsarin ajiyar kudin aikin hajji da wuri, ya shawarcesu da su amshi wasiko kan yawan kujeru da kuma lasisi na aikin hajjin 2025.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?
Manyan Labarai

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 
Manyan Labarai

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
Manyan Labarai

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Next Post
Sinawa 146 Dake Lebanon Sun Fice Daga Kasar Lami Lafiya

Sinawa 146 Dake Lebanon Sun Fice Daga Kasar Lami Lafiya

LABARAI MASU NASABA

2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.