• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Yanzu Saudiyya Ce Za Ta Kula Da Abincin Alhazan Nijeriya -NAHCON

byYusuf Shuaibu and Sulaiman
1 year ago
nahcon

Hukumar Kula Da Jin Dadin Alhazai ta Nijeriya (NAHCON) ta ce, hukumomi a kasar Saudi Arabiyya za su amshi ragamar kula da ciyar da maniyyata da samar musu da masauki a Makka da Madina, lamarin da zai fara kasancewa daga aikin hajjin 2025.

A wata sanarwar da kakakin NAHCON, Fatima Usara, ta fitar a makon jiya, ta ce, an cimma wannan fahimtar juna ne a wani tattaunawa ta yanar gizo da aka gudanar a tsakanin hukumar da ma’aikatar kula da aikin hajji da Umrah (MoHU) ta kasar Saudiyya.

  • Kaso 40 Na ‘Yan Nijeriya Na Samun Wutar Lantarki Fiye Da Awa 20 A Kowace Rana — Minista
  • APC Ta Lalata Nijeriya, PDP Kuma Matacciyar Jam’iyya Ce — Kwankwaso

Fatima ta kuma kara da cewa hukumar ta gudanar da ganawar fara shirye-shiryen gudanar da aikin hajjin da ke tafe da manyan sakatarorin kula da jin dadin alhazai na jihohi, wanda kwamishina a NAHCON, Anofi Elegushi ya jagoranta a ranar 23 ga watan Satumba.

A cewarta, Elegushi ya ce kamfanonin da hukumar alhazan Saudiyya ta assasa da aka fi sani da ‘mu’assasa’, su ne za su kula da ciyar da alhazai da samar musu da masauki a Makkah da Madina da zai fara daga 2025 bisa kulawar ma’aikatar MoHU.

“Wannan tsarin zai shafi dukkanin kasashen da za su halarci aikin hajji, kuma zai fara ne daga aikin hajjin 2025,” ya shaida.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Elegushi ya jaddada aniyar NAHCON na fara gudanar da shirye-shiryen aikin hajji bisa lokacin da Saudiyya ta bayar, kuma ya yi kira ga dukkanin masu ruwa da tsaki kan aikin hajji da su bayar da hadin kai.

Shugaban kungiyar jagororin hukumomin jin dadin alhazai na jihohi, Idris Almakura ya yaba wa NAHCON kan kokarinta da take kan yi, ya roki hukumar da ta ci gaba da daukan kyawawan tsare-tsaren da take bi.

Almakura ya nuna damuwarsa kan tsarin ajiyan kudin kujera, tsarin tawagar jami’an kiwon lafiya da kuma tsarin jinkirin maida wa maniyyata kudadensu.

Da yake maida jawabi, Elegushi ya yaba wa jagororin kula da aikin hajji na jihohi kan yunkurinsu na sanar da tsarin ajiyar kudin aikin hajji da wuri, ya shawarcesu da su amshi wasiko kan yawan kujeru da kuma lasisi na aikin hajjin 2025.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Sinawa 146 Dake Lebanon Sun Fice Daga Kasar Lami Lafiya

Sinawa 146 Dake Lebanon Sun Fice Daga Kasar Lami Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version