• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Yanzu Saudiyya Ce Za Ta Kula Da Abincin Alhazan Nijeriya -NAHCON

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
7 months ago
in Labarai
0
nahcon
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula Da Jin Dadin Alhazai ta Nijeriya (NAHCON) ta ce, hukumomi a kasar Saudi Arabiyya za su amshi ragamar kula da ciyar da maniyyata da samar musu da masauki a Makka da Madina, lamarin da zai fara kasancewa daga aikin hajjin 2025.

A wata sanarwar da kakakin NAHCON, Fatima Usara, ta fitar a makon jiya, ta ce, an cimma wannan fahimtar juna ne a wani tattaunawa ta yanar gizo da aka gudanar a tsakanin hukumar da ma’aikatar kula da aikin hajji da Umrah (MoHU) ta kasar Saudiyya.

  • Kaso 40 Na ‘Yan Nijeriya Na Samun Wutar Lantarki Fiye Da Awa 20 A Kowace Rana — Minista
  • APC Ta Lalata Nijeriya, PDP Kuma Matacciyar Jam’iyya Ce — Kwankwaso

Fatima ta kuma kara da cewa hukumar ta gudanar da ganawar fara shirye-shiryen gudanar da aikin hajjin da ke tafe da manyan sakatarorin kula da jin dadin alhazai na jihohi, wanda kwamishina a NAHCON, Anofi Elegushi ya jagoranta a ranar 23 ga watan Satumba.

A cewarta, Elegushi ya ce kamfanonin da hukumar alhazan Saudiyya ta assasa da aka fi sani da ‘mu’assasa’, su ne za su kula da ciyar da alhazai da samar musu da masauki a Makkah da Madina da zai fara daga 2025 bisa kulawar ma’aikatar MoHU.

“Wannan tsarin zai shafi dukkanin kasashen da za su halarci aikin hajji, kuma zai fara ne daga aikin hajjin 2025,” ya shaida.

Labarai Masu Nasaba

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

Elegushi ya jaddada aniyar NAHCON na fara gudanar da shirye-shiryen aikin hajji bisa lokacin da Saudiyya ta bayar, kuma ya yi kira ga dukkanin masu ruwa da tsaki kan aikin hajji da su bayar da hadin kai.

Shugaban kungiyar jagororin hukumomin jin dadin alhazai na jihohi, Idris Almakura ya yaba wa NAHCON kan kokarinta da take kan yi, ya roki hukumar da ta ci gaba da daukan kyawawan tsare-tsaren da take bi.

Almakura ya nuna damuwarsa kan tsarin ajiyan kudin kujera, tsarin tawagar jami’an kiwon lafiya da kuma tsarin jinkirin maida wa maniyyata kudadensu.

Da yake maida jawabi, Elegushi ya yaba wa jagororin kula da aikin hajji na jihohi kan yunkurinsu na sanar da tsarin ajiyar kudin aikin hajji da wuri, ya shawarcesu da su amshi wasiko kan yawan kujeru da kuma lasisi na aikin hajjin 2025.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Adawa Da Kara Haraji Da EU Ta Yi Kan Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin

Next Post

Sinawa 146 Dake Lebanon Sun Fice Daga Kasar Lami Lafiya

Related

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

55 minutes ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

4 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

5 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

5 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

6 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

8 hours ago
Next Post
Sinawa 146 Dake Lebanon Sun Fice Daga Kasar Lami Lafiya

Sinawa 146 Dake Lebanon Sun Fice Daga Kasar Lami Lafiya

LABARAI MASU NASABA

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.