Dakarun Sojin Nijeriya tare da haɗin gwiwar Civilian JTF da mafarauta, sun daƙile wani hari da ISWAP suka kai Dikwa, garin da ke maƙwabtaka da Marte.
Wani ɗan CJTF da ya buƙaci a sakaya sunansa ya ce, ‘yan ta’addan sun fara aika jiragen leƙen asiri guda biyu kafin su kai harin da misalin ƙarfe 1 na dare a wani shingen sojoji.
- Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi
- Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci
Ya ce harin ya ɗauki kusan awa ɗaya, inda sojoji da CJTF suka mayar da martani inda suka dinga ɗauki ba daɗi.
“Ina ganin sun biyo sojojinmu da suka janye daga Marte, amma wannan karon, sojojinmu sun yi ƙoƙari sosai wajen kare garin,” in ji shi.
A ranar Litinin ne, ‘yan ta’adda suka hari garin Marte da ke Jihar Borno, inda suka hallaka sojoji tare da raunata wasu.
A yanzu haka ana zargin wasu dakarun sojin sun ɓace tun bayan kai harin na ranar Litinin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp