• English
  • Business News
Tuesday, June 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dakataccen Malamin Kwaleji Ya Dawo Karen Mota A Ribas

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Dakataccen Malamin Kwaleji Ya Dawo Karen Mota A Ribas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dakataccen Malamin Kwalejin Kimiyya da fasaha ta Captain Elechi Amadi Polytechnic da ke Fatakwal a jihar Ribas, Mista Zoe Solomon Tamunotonye, ya koma karen mota domin neman taro da sisin da zai ciyar da kansa biyo bayan kin biyansa albashinsa na sama da watanni shida da Kwalejin ta ki yi.

A wani faifan bindiyo da aka yada a kafafen sada zumunta, an ga Tamunotonye na gwagwarmayar neman fasinjoji da su shiga motar kabu-kabu a kan hanyar Ikwerre da ke garin Fatakwal babban birnin jihar Ribas.

  • Lalata Da ‘Yar Shekara 14: Kotu Ta Daure Jarumin Nollywood Baba Ijesha Shekara 16 A Gidan Yari

Shi dai malamin kwalejin, hukumar gudanarwar ta Kwalejin ce ta dakatar da shi biyo bayan rahoton da kwamitin da aka kafa domin bincikensa kan zargin lalata da wata dalibar Kwalejin.

Tirka-tirkar alakar da ke tsakaninsa da dalibar har sai da ta kai ga ‘yan sanda sun tsare ita dalibar a caji ofis din Sani Abacha da ke garin na Fatakwal.

Malamin ya dawo ya zargi dalibar da karkatar da kudin da ya kai naira N250,000 da ya bata domin yin kasuwanci kuma ta rike masa makullin ofis da wasu kadarorinsa.

Labarai Masu Nasaba

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

Daga baya ne kuma kwamishinan ‘yan sanda Eboka Friday ya shiga cikin lamarin da har aka sake dalibar bisa cewa bayan da ya saurari dukkanin bangarorin da abun ya shafa, ya gano zargin da malamin ke yi babu sahihin gaskiya a ciki.

Idan za a iya tunawa dai Kwalejin ta Captain Elechi Amadi Polytechnic a watan Maris na 2022 ta fitar da sanarwar na cewa ta samu Zoe Solomon Tamunotonye dumu-dumu kan zarginsa da ake yi da rashin da’a gami da cin zarafin dalibar.

Sanarwar wacce Rijistan Kwalejin Chris Woke ya sanya wa hannu inda suka bai wa malamin Kwalejin zuwa ranar 31 ga watan Mayun 2022 da ya rubuta wasikar neman afuwa da yafiyar Kwalejin tare da daukan alkawarin zai zama daga cikin malamai masu cikakken da’a da ladabi.

Sai dai Malamin ( Zoe Solomon) ya ki rubuta neman yafiyar bisa nashi ra’ayin na cewa shi fa atafau bai aikata laifin komai da zai sanya shi rubuta ban hakuri da neman gafara ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Ba Da Gudummawar Dala Miliyan 50 Ga Asusun Yaki Da Annoba Na Bankin Duniya

Next Post

Budurwa Ta Gudu Da Motar Saurayinta Bayan Ya Je Saya Mata Shawarma A Kano

Related

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran
Kasashen Ketare

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

1 hour ago
Sirikin Buhari Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Kaduna
Manyan Labarai

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

2 hours ago
Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano

6 hours ago
Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe
Labarai

Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

14 hours ago
Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake
Labarai

Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake

16 hours ago
Next Post
Budurwa Ta Gudu Da Motar Saurayinta Bayan Ya Je Saya Mata Shawarma A Kano

Budurwa Ta Gudu Da Motar Saurayinta Bayan Ya Je Saya Mata Shawarma A Kano

LABARAI MASU NASABA

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

June 17, 2025
Sirikin Buhari Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Kaduna

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

June 17, 2025
Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

June 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano

‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano

June 17, 2025
Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

June 16, 2025
Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda

Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda

June 16, 2025
Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

June 16, 2025
Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

June 16, 2025
Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara

Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara

June 16, 2025
Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake

Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake

June 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.