• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dakta Olusola Saraki: Shekara 10 Da Rasuwar Dattijon Arziki, Baya Goya Marayu

by Bello Hamza
3 years ago
in Manyan Labarai, Masarautu
0
Dakta Olusola Saraki: Shekara 10 Da Rasuwar Dattijon Arziki, Baya Goya Marayu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Litinin 28 ga watan Nuwamba 2022 ne ‘yanuwa, iyalai da abokan siyasar Marigayi Dakta Abubakar Olusola Saraki (Turakin-Ilori) wanda aka fi sani da Oloye suka taru a babban dakin taro na Chida Otel da ke Abuja don tunawa da cika shekara 10 da rasuwarsa, an gudanar da taron ne a kakashin jagorancin Sarkin Musulmi Mai Martaba Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar 111 yayin da Sarkin Ilori Mai Martaba Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari ya jagoranci tawagar Sarakunan gargajiyar da suka samu halartar taron, yayin da shaharren mai jawabin nan wanda ya shahara a Afrika, Farfesa P L O Lumumba ya gabatar da jawabi inda ya gabatar da mukala mai taken ‘Muhawarar A Kan Shugabanni Da Mabiya A Afrika’.

Taron ya dauki wani sabon salo musamman ganin ana gudanar da shi ne a daidai lokacin da ake tsaka da gangamin tarukkan yakin neman zabe a sassan kasar nan na wadanda za su cike gurbin shugabanaci a shekarar 2023, amma maimakon masu shirya taron su mayar da dandalin taron ya zama tamkar wajen yakin neman zabe ko kuma wajen da za su tallata ‘yan takarar su amma sai gashi sun gaiyato kusan ‘yan siyasa daga dukkan bangarorin siyasar kasar nan, domin a hadu a kan akidar siyasar Marigayi Oloye ta kishin kasa da tabbagtar da cigaban ta.

  • 2023: Muradun CAN Da Na Dattawan Arewa A Sikeli
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Hanyar Abuja Zuwa Kogi

A jawabinsa na maraba, daya daga cikin manyan ‘yan’yan Marigayi Sola Saraki, Tsohon shugaban majalisar Dattawa, Dakta Abubakar Bukola Saraki, ya bayyana cewa, dalilin wannan shi ne na ganin cewa, Marigayin yana da magoya baya da wadanda ya yi tasiri a rayuwarsu a kusan dukkan siyasun kasar nan a kan haka zai zama tamkar rashin mutunci gare shi a ware wasu ‘yan siyasa a irin wannan taron. Ya ce, Mahaifinsu ya rungumi al’umma daga dukkan bangarorin kasar nan ba tare da nuna banbacin addini ko kabilanci ba, “Wannan akidar ce ta sanya a kusan dukkan inda ka ambaci sunansa sai ka samu wanda zai bayar da shaidar wani abin alhairin da ya aikata tare da kuma yi masa addu’a, mu da kanmu iyalansa har yanzu muna cigaba da amfana da ayyukan alhairin da ya gabatar a zamanin rayuwarsa, za kuma mu cigaba da amfana har zuwa ‘ya’ya da jikokinmu, saboda haka muke kira ga al’ummar Nijeriya su rungumi halayya irin ta Dakta Abubakar Olusola Saraki ta haka za a samu kasa mai cike kwanciyar hankali da son juna.’’ In ji shi.

A nasa jawabin a matsayinnsa na shugaban taron, Sarkin Musulmi Alhaji Abubakar Sa’ad ya tuno da lokacin da ya fara saduwa da Marigayi Sola Saraki a lokacin yana aikin soja a mukamin Kaftin a barikin Soja da ke Ilori, ya ce, tun a lokacin ya fahinci mutunci da dattakunsa daga nan ne kuma suka kulla kyakyawar alaka da iyalan Marigayin har zuka wannan lokacin. Al’umma da dama na cigaba da kewar Marigayin ne saboda irin ayyyukan al’hairin da ya shuka wadanda suka hada bayar da tallafin karatu ga yaran talakawa da koya wa yaran talakawa sana’o’in dogaro da kai, wanda haka ya sa har zuwa yanzu sunansa bai bace a zukatan al’umma ba saboda yadda ya rike su a matsayin ‘ya’yansa. Daga nan ya shawarci zuriyyar da Marigayin ya bar a karkashin jagorancin Dakta Bukola Saraki, Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa da su tabbatar da sun rungumi akidun marigayyin, ‘Ta haka ne sunansa zai cigaba da wanzuwa” in ji shi.

A mukalar da ya gabatar, mai take “Muhawara a Kan Shugabanci da Magoya baya’ Farfesa LPO Lumumba ya yi dogon tsokaci ne a kan yadda Afrika ta fada cikin matsalar shugabanci da kuma yadda magoya baya suka kasa fahintar alhakin da ke kansu na tsayuwa tare da tsawata wa shugabanni a yayin da suka kauce hanyar da ya kamata na bunkasa rayuwar al’umma, ya ce, tun da farko Turawan Mulkin mallaka basu shirya barin tafiyar da harkokin mulkin kasashen Afrika ba, a kan haka suka dora kasashen a kan tafarkin da za su cigaba da tsoma baki a kan yadda ake tafiyar da harkokin kasa duk kuwa da sun bar mukin a hannun ‘yan kasashen Arikan ne a zahiri amma sune ke tsarawa sune kuma suke bayar da yadda za a gudanar da komai, a kan haka ne suka kafa kungiyoyi irin su na kasashe renon Birtaniya da irin na kasashe renon Faransa” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

Ya ce, dole shugabannin Afrika a wananan lokaci su farka su kuma yi koyi da halaye irin su na Marigayi Sola Saraki wadanda suka sanya cigaban al’ummar su fiye da komai, “Ta hake ne kawai al’ummar kasashen Afrika za su kubuta daga kangin Turawan Mulki Mallaka duk kwa da sun ba kasashen mu mulkin kai fiye da shekaru 60 da suka wuce’, in ji shi.

An dai haifi Dakta Abubakar Olusola Saraki ne a a ranar 17 ga wata Mayu na shekarar 1933 ya auri Misis Florence Morenike Saraki suna da ‘ya’ya hudu, sun kuma hada da Dakta Abubakar Bukola Saraki Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa kuma tsohon Gwamnan Jihar Kwara har sau biyu da Sanata Rukayat Gbemisola Saraki wadda ta taba zama mamba a majalisar wakilai a halin yanzu kuma ita ce Ministar ma’adanai da Misis Fatimoh Temitope Edu (Nee Saraki) wadda a halin yanzu tana harkokin kasuwancinta ne a Legas sai kuma na karshe, Mista Mutairu Olaolu Saraki, wanda ya taba yi wa marigayi tsohon shugaban kasa Umaru Musa ‘Yar’adua mataimaki na musamman. Dakta Sola Saraki ya rasu ne a ranar 14 ga watan Nuwamba 2012 yana da shekara 79 a duniya.

Cikin abubuwan da aka shiya don tunawa da cikarsa shekasra 10 da rasuwa, akwai bayar da tallafin magani kyauta ga mabukata a garin Ilori, kaddamar da littafin tarihinsa wanda aka sama suna ‘’Sola Saraki: The Stateman’’, littafin na kunshe ne da tarihin gwagwamayar rayuwarsa na siyasa da yadda ya yi watsi da aikinsa na Likita ya rungumi siyasa da mukaman da ya rike har zuwa lokacin da ya zama Jagoran Majalisar Dattawa a jamhoriyya ta 2, lokacin Alhaji Shehu Shagari ke mulki.

Taron ya samu halartar manyan ‘yan siyasa daga dukkan bangarorin siyasar kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Baya Goya MarayuMarigayiSarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

Next Post

An Tsinci Gawar Wani Dan Kasuwa Mai Shekaru 37 A Otel A Jihar Bauchi

Related

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

10 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Da ɗumi-ɗuminsa

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

12 hours ago
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja
Manyan Labarai

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

14 hours ago
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno
Manyan Labarai

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

16 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

2 days ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

2 days ago
Next Post
An Tsinci Gawar Wani Dan Kasuwa Mai Shekaru 37 A Otel A Jihar Bauchi

An Tsinci Gawar Wani Dan Kasuwa Mai Shekaru 37 A Otel A Jihar Bauchi

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.