• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalibai Miliyan 1.4 Da Suka Rubuta Jarra-bawar UTME Sun Ci Maki Kasa Da 200

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
UTME
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar shirya jarabawar sharar fagen shiga manyan makarantu a kasar nan (JAMB), a ranar Litinin da ta gabata ta sake sakamakon jarabawar na shekarar 2024, inda sakamakon ya nuna cewa dalibai 1,402,490 daga cikin 1,842,464 sun kasa iya cin maki 200 daga cikin maki 400 na jarabawar.

Adadin daliban da suka kasa cin sakamakon sun dauki kaso 78 cikin dari na duk-kanin daliban da suka zauna domin rubuta jarabawar kamar yadda sakamakon da JAMB ta fitar ya nuna.

  • JAMB Ta Fitar Da Sakamakon Jarrabawar 2024, Sakamako 64,624 Na Karkashin Bincike
  • UTME: JAMB Ta Ba Da Umurnin Kamo Iyayen Da Aka Gansu Kusa Da Cibiyoyin Zana Jarabawa

Da yake bayar da bayani kan sakamakon jarabawar dalibai 1,842,464, Rajistara na hukumar, Farfesa Ishak Oloyede, ya ce, “Dalibai 8,401 ne kawai suka iya samun maki 300 ko fiye da haka, dalibai 77,070 sun ci maki 250 ko fiye, sai kuma 439,974 da suka ci maki 200 ko fiye, yayin da kuma dalibai 1,402,490 suka ci maki kasa da 200.”

Ya ce, hukumar ba ta saba wallafa sunayen wadanda suka yi zarra a jarabawar ba, illa iyaka tana fito da jerin yadda sakamakon ya kaya.

A gefe guda, shugaban hukumar ya nemi al’umma da ka da su sake fadawa irin tarkon da Mmesoma ta taba jefa wasu, inda ya ce a kowani lokaci wani ko wata daliba suka yi ikirarin samun wasu sakamakon jarabawar mai gwabi, kafin mutane su dukufa wajen musu kyautuka su nemi tabbaci daga hukumar domin kauje wa shiga kokonto.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

Oloyede ya kuma ce an rike sakamakon jarabawar dalibai 64,624 daga cikin wadanda suka zana jarabawar, inda ake kan gudanar da bincike kan zargin satan amsa, sahihancin cibiyar zana jarabarsu da dai sauransu.

A cewarsa, adadin daliban da suka yi rajistan zana jarabawar sun kai 1,989,668, inda a cikin dalibai 80,810 ba su je sun zana jarabawar ba, “Adadin dalibai 1,904,189 ne suka zauna domin zana jarabar UTME a cikin kwanaki shida.”

Oloyede ya ce hukumar ta shirya wa daliban da suke kasashen waje jarabawa a wurare tara da suka hada da Abidjan, Ibory Coast; Addis Ababa, Ethiopia; Buea, Cameroon; Cotonou, jamhuriyyar Benin; London, Burtaniya; Jeddah, Saudi Ara-bia; da Johannesburg, Afrika ta Kudu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ASUUJambUTME
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Hanyoyin Ruwa Suka Zama Tarkunan Mutuwa A Nijeriya

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

36 minutes ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

2 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

5 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

6 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

15 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

18 hours ago
Next Post
Goro

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.