ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalibai Sun Bukaci Tinubu Da Gwamnoni Da Su Kula Da Sha’anin Tsaro, Ilimi Da Wutar Lantarki

by Muhammad
2 years ago
Dalibai

A jiya Juma’a ne daliban Nijeriya suka bi sahun tsari da kudurorin gwamnati mai jiran gado take fatan zuwa da shi, inda suka bukaci zababben shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya tabbatar da ingantaccen tsaro da samar da ingantaccen ilimi a gwamnatinsa.

Har ila yau, a cikin jerin bukatun da suka gabatar a gaban gwamnati mai zuwa akwai samar da tsayayyiyar wutar lantarki da kuma dabarun yaki da dakile yunwa da fatara da daukaka darajar Nijeriya ta hanyar amfani da kyawawan manufofi.

  • Ku Zabi Tunibu Na Yi Imani Zai Dora Daga Inda Na Tsaya — Buhari
  • Kwana 4 Ga Rantsuwa: Yadda Shugabannin Duniya Ke Tururuwar Rantsar Da Tinubu

Galibin yaran Nijeriya, wasu na ta gararanba a kan tituna, suna fuskantar matsalolin damuwa da shaye-shayen miyagun kwayoyi, safarar mutane, fyade, tashin hankali talauci da dai sauransu.

ADVERTISEMENT

Wani bangare na daliban da suka zanta da manema labarai a fadin kasar, sun yi kira ga Tinubu da ya magance matsalar rashin tsaro, musamman a makarantu da samar da yanayin da daliban da suka rasa matsugunansu za su koma makaranta.

Yaran ‘yan makarantar sun koka da cewa a halin yanzu yawancinsu suna karatu a cikin yanayi na tsoro da rashin tabbas, wanda hakan ke jawo musu rugujewar tunani saboda tsoron abin da ba a sani ba.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Daliban da suka yi magana game da abin da suke sa rai daga gwamnati mai zuwa a wani bangare na ayyukan tunawa da ranar yara ta bana, sun kuma bukaci Tinubu da ya gaggauta sake fasalin Nijeriya musanman yaki da yunwa.

Daliban sun kuma roki gwamnatin tarayya da ta ci gaba da gudanar da shirin ciyar da makarantu na kasa domin bunkasa ilimin boko da bunkasa noma.

A wata tattaunawa da suka yi da LEADERSHIP, daliban sun bukaci gwamnati mai jiran gado da ta magance matsalolin da ke hana yara zuwa makaranta, wanda ya haifar da yara sama da miliyan 20 da ba sa zuwa makaranta.

A Abuja, wasu yaran ‘yan makaranta da suka zanta da wakilinmu sun roki gwamnatin da ta magance matsalar sace yara ‘yan makaranta da ta addabe su, tare da ba su kariya a matsayinsu na shugabannin Nijeriya a gobe.

Wata dalibar Sakandaren Gwamnati Garki da ke Abuja, Emmanuel Pamela, ta ce kalubalen farko da za ta so gwamnati ta tunkara shi ne rashin tsaro.

Pamela ta ce, “Na tabbata kowa na son Nijeriya da inda yake aiki, zai ji dadi matsawar aka samu zaman lafiya da kwanciyar hankali.

“Ina son gwamnati mai zuwa ta tabbatar da cewa dukkan yara suna makaranta tare da tabbatar da tsaro ga yaran.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule
Manyan Labarai

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista
Manyan Labarai

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Next Post
Kwana 2 Kafin Rantsuwa: Kotun Koli Ta Yi Watsi Da Karar PDP Kan Takarar Tinubu Da Shettima

Kwana 2 Kafin Rantsuwa: Kotun Koli Ta Yi Watsi Da Karar PDP Kan Takarar Tinubu Da Shettima

LABARAI MASU NASABA

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

November 13, 2025
Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

November 13, 2025
Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

November 13, 2025
‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.