• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalibai Sun Bukaci Tinubu Da Gwamnoni Da Su Kula Da Sha’anin Tsaro, Ilimi Da Wutar Lantarki

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Dalibai Sun Bukaci Tinubu Da Gwamnoni Da Su Kula Da Sha’anin Tsaro, Ilimi Da Wutar Lantarki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Juma’a ne daliban Nijeriya suka bi sahun tsari da kudurorin gwamnati mai jiran gado take fatan zuwa da shi, inda suka bukaci zababben shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya tabbatar da ingantaccen tsaro da samar da ingantaccen ilimi a gwamnatinsa.

Har ila yau, a cikin jerin bukatun da suka gabatar a gaban gwamnati mai zuwa akwai samar da tsayayyiyar wutar lantarki da kuma dabarun yaki da dakile yunwa da fatara da daukaka darajar Nijeriya ta hanyar amfani da kyawawan manufofi.

  • Ku Zabi Tunibu Na Yi Imani Zai Dora Daga Inda Na Tsaya — Buhari
  • Kwana 4 Ga Rantsuwa: Yadda Shugabannin Duniya Ke Tururuwar Rantsar Da Tinubu

Galibin yaran Nijeriya, wasu na ta gararanba a kan tituna, suna fuskantar matsalolin damuwa da shaye-shayen miyagun kwayoyi, safarar mutane, fyade, tashin hankali talauci da dai sauransu.

Wani bangare na daliban da suka zanta da manema labarai a fadin kasar, sun yi kira ga Tinubu da ya magance matsalar rashin tsaro, musamman a makarantu da samar da yanayin da daliban da suka rasa matsugunansu za su koma makaranta.

Yaran ‘yan makarantar sun koka da cewa a halin yanzu yawancinsu suna karatu a cikin yanayi na tsoro da rashin tabbas, wanda hakan ke jawo musu rugujewar tunani saboda tsoron abin da ba a sani ba.

Labarai Masu Nasaba

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

Daliban da suka yi magana game da abin da suke sa rai daga gwamnati mai zuwa a wani bangare na ayyukan tunawa da ranar yara ta bana, sun kuma bukaci Tinubu da ya gaggauta sake fasalin Nijeriya musanman yaki da yunwa.

Daliban sun kuma roki gwamnatin tarayya da ta ci gaba da gudanar da shirin ciyar da makarantu na kasa domin bunkasa ilimin boko da bunkasa noma.

A wata tattaunawa da suka yi da LEADERSHIP, daliban sun bukaci gwamnati mai jiran gado da ta magance matsalolin da ke hana yara zuwa makaranta, wanda ya haifar da yara sama da miliyan 20 da ba sa zuwa makaranta.

A Abuja, wasu yaran ‘yan makaranta da suka zanta da wakilinmu sun roki gwamnatin da ta magance matsalar sace yara ‘yan makaranta da ta addabe su, tare da ba su kariya a matsayinsu na shugabannin Nijeriya a gobe.

Wata dalibar Sakandaren Gwamnati Garki da ke Abuja, Emmanuel Pamela, ta ce kalubalen farko da za ta so gwamnati ta tunkara shi ne rashin tsaro.

Pamela ta ce, “Na tabbata kowa na son Nijeriya da inda yake aiki, zai ji dadi matsawar aka samu zaman lafiya da kwanciyar hankali.

“Ina son gwamnati mai zuwa ta tabbatar da cewa dukkan yara suna makaranta tare da tabbatar da tsaro ga yaran.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Daliban NijeriyaGwamnoniRanar YaraTunibu
ShareTweetSendShare
Previous Post

“Magance Hadari”? “Raba Gari Ta Fannin Tattalin Arziki Da Sin Shi Ne Hadari

Next Post

Kwana 2 Kafin Rantsuwa: Kotun Koli Ta Yi Watsi Da Karar PDP Kan Takarar Tinubu Da Shettima

Related

Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Manyan Labarai

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

54 minutes ago
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

5 hours ago
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

8 hours ago
Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

19 hours ago
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

23 hours ago
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

1 day ago
Next Post
Kwana 2 Kafin Rantsuwa: Kotun Koli Ta Yi Watsi Da Karar PDP Kan Takarar Tinubu Da Shettima

Kwana 2 Kafin Rantsuwa: Kotun Koli Ta Yi Watsi Da Karar PDP Kan Takarar Tinubu Da Shettima

LABARAI MASU NASABA

Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.