ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwana 4 Ga Rantsuwa: Yadda Shugabannin Duniya Ke Tururuwar Rantsar Da Tinubu

by Sadiq
3 years ago
Tinubu

Gabanin bikin rantsar da zababben shugaban kasar Nijeriya, Bola Tinubu a ranar 29 ga watan Mayu, babbar hukumar Birtaniya a Abuja ta bayar da jadawalin wata tawaga da za ta halarci bikin.

Shugaban sashen yada labarai na hukumar kolin Birtaniya da ke Abuja, Dean Hurlock ne ya bayyana hakan a ranar Laraba.

  • Mun Yi Iya Kokarinmu Wajen Shugabancin Nijeriya —Buhari
  • LEADERSHIP Da CMG Sun Karfafa Dangantakar Aiki A Tsakaninsu

Ya ce, “Tawagar ta Birtaniya za ta kasance karkashin jagorancin Firaminista Andrew Mitchell MP, Karamin Ministan Ci Gaban Afirka a Ofishin Harkokin Waje, tare da Wakilin Fira Ministan Harkokin Kasuwanci a Nijeriya sa kuma Wakili na Musamman kan Ilimin ‘Yara Mata, Helen Grant (OBE, MP) da Babban Kwamishinan Birtaniya a Nijeriya, Dokta Richard Montgomery, CMG.”

ADVERTISEMENT

A halin da ake ciki kuma, haifaffen Nijeriya Enoh Ebong na cikin tawagar Amurka da za ta halarci bikin rantsar da zababben shugaban kasa Bola Tinubu a ranar 29 ga watan Mayu.

Ebong na cikin tawagar wakilai tara da shugaban Amurka Joe Biden ya sanar a ranar Litinin.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Wata sanarwa da ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja ya fitar a ranar Talata, ta ce tawagar za ta kasance karkashin Sakatariyar Gidaje da Raya Birane ta Amurka, Marcia L. Fudge.

Sauran mambobin tawagar Amurka zuwa Nijeriya sun hada da: David Greene, mai kula da ofishin jakadancin Amurka a Abuja; Sydney Kamlager-Dove.

Wakili daga California; Marisa Lago, ma’aikatar kasuwanci ta Amurka, ma’aikatar kasuwanci ta kasa da kasa, da kuma Michael E. Langley, kwamandan rundunar Amurka a Afrika.

Sauran sun hada da Mary Catherine Phee, Mataimakiyar Sakatariyar Harkokin Wajen Amurka kan Harkokin Afirka; Judd Devermont, mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin tsaro na kasa kuma babban darakta mai kula da harkokin Afirka, da Monde Muyangwa, mataimakiyar mai kula da harkokin Afirka a hukumar raya kasashe ta Amurka (USAID).

Kwanan nan Ebong ta jagoranci tawagar binciken Amurka zuwa Nkjeriya da Ruwanda domin inganta harkokin kasuwanci da zuba jari a kasashen.

Enoh Ebong, wadda ita ce mataimakin daraktar hukumar kasuwanci da raya kasa ta Amurka, ta samu rakiyar sakatariyar kasuwanci ta Amurka, Penny Pritzker, da mambobin kwamitin ba da shawara na shugaban kasa kan harkokin kasuwanci a Afirka.

Da yake tsokaci kan aikin, Ebong ta ce an tsara aikin ne domin musayar bayanai da kuma gano damammaki na inganta huldar kasuwanci tsakanin Amurka da Afirka.

Ta ce, “An nemi na shiga cikin wannan tafiya a matsayina na mataimakiyar daraktan ciniki na Amurka da

Hukumar Raya Kasa, wacce ke hada kai da kamfanonin Amurka don tsara hanyoyin magance kalubalen ci gaba a Nijeriya, Rwanda da ma duniya baki daya.

“Muhimmin abu ne na abin da muke yi. A cikin muhimman matakai na farko na ci gaban aikin samar da ababen more rayuwa, muna gina hadin gwiwa tsakanin masu ruwa da tsaki na Afirka da kamfanonin Amurka wadanda ke gano abubuwan da suka dace don tabbatuwar aikin.”

Ta bayyana cewa, a lokacin da ta fara zuwa USTDA, a kwanan baya gwamnatin Nijeriya ta fara bude bangaren sadarwa.

Tun daga wannan lokacin, ta ce Amurka na hada kamfanonin sadarwa na Nijeriya da kwararrun Amurka wadanda za su taimaka musu wajen sabunta ababen more rayuwa.

“A halin yanzu muna taimaka wa Kamfanin Main One Cable na Nijeriya don shirin tsawaita hanyar sadarwa ta ‘fiber optic’ karkashin teku mai nisan mil 300 daga Legas zuwa Fatakwal, ta hanyar aikinsu tare da wani kamfani na Amurka, HIP Consult, Inc. (Washington, DC).

Aikin zai kara yawan mutane da kasuwancin da ke da damar yin amfani da sadarwa a duk yankin.

“Saboda wannan samfurin ya tabbatar da nasara sosai, muna amfani da shi ne don taimaka wa abokan huldar mu na Nijeriya su bunkasa bangaren wutar lantarkinsu. Muna aiki don kawo makamashi ga karin ‘yan Nijeriya. Misali daya shi ne, USTDA tana kimanta karfin fasaha da kudi na gina tashar wutar lantarki mai karfin megawatt 275.”

A cewarta, aikin zai kara karfi da kuma inganta samar da wutar lantarki ga abokan huldar zama da na kasuwanci a fadin Jihar Legas.”

“Wannan yunkurin babban misali ne na yadda Amurka da Afirka ke aiki tare don kara samar da wutar lantarki a karkashin shirin Shugaba Obama na ‘Power Africa’.

“Ta hanyar hada kai a kan ayyuka irin wannan, muna taimakawa wajen tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya da yawa sun samu damar samun makamashi. Kuma muna taimakawa wajen karfafa dangantakar tattalin arziki tsakanin Nijeriya da Amurka,” in ji ta.

Da ta ke magana a kan asalinta l, Ebong ta ce, “A matsayina na ’yar Nijeriya kuma ’yar kasar Amurka mai alfahari, na fara ganin yadda abubuwan da mahaifina ya yi a baya suka tsara rayuwata. Yunkurinsa na ci gaban Nijeriya ya sa na shiga cikin kokarin gwamnatin Amurka na bunkasa ci gaba ta hanyar amfani da kwarewa da albarkatun kamfanoni masu zaman kansu na Amurka.

“Ina matukar godiya da wannan damar na komawa kasar da aka haife ni da kuma shiga cikin masu ruwa da tsaki na Amurka da na Afirka wajen musayar ra’ayoyi don karfafa hadin gwiwarmu. Na san mahaifina zai yarda cewa, ta hanyar karfafa dangantakar kasuwanci da ci gaba a yau, muna taimakawa wajen tabbatar da kwanciyar hankali da wadata a gobe.”

A halin da ake ciki kuma, bayan bin sahun kasashen Amurka da Birtaniya, a jiya, kasar Kanada ta bayyana ta hannun babbar hukumarta cewa kasar za ta wakilci kasar a wajen bikin rantsar da Tinubu.

A nata bangaren, babbar hukumar Indiya da ke Abuja ta shaida wa wakilinmu a Abuja a jiya cewa, kasar za ta samu wakilcin tawaga.

Jami’in yada labarai na tawagar, Vipul Mesariya, ya shaida wa LEADERSHIP cewa, Delhi na iya tura wata tawaga karkashin jagorancin minista.

Hukumomin kasar Sin da ke ofishin jakadanci da ke Abuja sun kuma tabbatar da cewa, akwai yiyuwar wata tawagar gwamnatin kasar Sin za ta halarci taron, domin nuna goyon baya ga Nijeriya, da karfafa dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu.

Jami’in kula da harkokin siyasa da yada labarai, Gu Jing, ya shaida wa wakilinmu cewa, tabbas kasar za ta aiko da wakili, amma har yanzu babu tabbas.

Wata majiya daga Saliyo ta shaida wa wakilinmu a jiya cewa, akwai yiwuwar shugaban kasar Julius Mada Bio, ya jagoranci wata tawaga zuwa rantsar da Tinubu.

Ofishin jakadancin Turkiyya ya kuma shaida wa LEADERSHIP cewa har yanzu ana kan hada tawagar da za a aiko Nijeriya.

Wata majiya a ofishin jakadancin da ba ta bayyana sunanta ba, ta ce mai yiwuwa a sanar da tawagar kafin karshen mako.

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ayyana Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairun 2023.

Ya doke abokan hamayyarsa Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP da Peter Obi na jam’iyyar LP, inda ya lashe kujerar da Nijeriya mafi girma.

Sai dai kuma, Atiku da Peter Obi ne ke kalubalantar nasarar da Tinubu ya samu a kotun sauraren kararrakin zabe, inda suka yi zargin cewa hukumar zaben ta yi magudin zabe ne domin fifita tsohon gwamnan ja Jihar Legas.

Har ila yau, sun yi zargin cewa Tinubu na da alaka da harkar safarar miyagun kwayoyi a Amurka.

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
An Gurfanar Da Tsohon Mataimakin Kakakin Majalisar Ogun Kan Zargin Tada Zaune-Tsaye

An Gurfanar Da Tsohon Mataimakin Kakakin Majalisar Ogun Kan Zargin Tada Zaune-Tsaye

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.