• English
  • Business News
Monday, May 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daliban Jami’ar Jos 6 Da Aka Sace Sun Shaki Iskar ‘Yanci

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Daliban Jami’ar Jos 6 Da Aka Sace Sun Shaki Iskar ‘Yanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shida daga cikin dalibai bakwai na jami’ar Jos da aka yi garkuwa da su, sun tsira bayan shafe kwanaki biyu a hannun masu garkuwa da mutane.

Daliban wadanda suke rayuwa a kusa da makarantar a daren ranar Laraba da daddare ne ‘yan bindigan suka kutsa kai cikin dakunansu da ke kan hanyar Bauchi ta layin Ring da ke karamar hukumar Jos ta arewa inda suka yi awun gaba da su.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Daliban Jami’ar Jos 7
  • Dan Majalisar Dokokin Jihar Legas, Abdulsobur Omititi Ya Rasu A Wajen Taron Tinubu A Jos 

Kwamishinan ‘yansandan jihar Filato, shi ne ya sanar da batun kubutar daliban a wata sanarwar da ya fitar, ya ce, rundunar tana kan kokarin ceto sauran dayan dalibin.

Sanarwar ta ce, “A yau, rundunar ‘yansandan jihar Filato tana farin cikin sanar da al’umma cewa biyar daga cikin daliban da aka yi garkuwa da su a ranar 13/06/2023 sun samu ‘yancinsu.

“Rundunar ta dauki matakan gaggawa tun lokacin da ta samu labarin garkuwan kuma bisa aiki tukuru da sashin yaki da masu garkuwa da mutane, iyalan wadanda lamarin ya shafa da al’umma domin tabbatar da an kubutar da daliban.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe

“Daya daga cikin daliban ya tsere daga hannun masu garkuwan, har yanzu kuma akwai sauran mutum daya a hannun masu garkuwan. Adadin wadanda suka kubutar zuwa yanzu su shida (6) ke nan.

“Kazalika, kwamishinan ‘yansanda Bartholomew N. Onyeka ya bayar da umarni ga kwamandan yankin Metro da babban baturen ‘yansansa (DPO) a caji ofis din Nasarawa Gwong da su tabbatar sun ceto dayan dalibin daga hannun masu garkuwan tare da kamosu domin su fuskanci hukunci daidai da laifinsu.”

Kwamishinan ya nanata aniyar hukumar na kare rayuwa da dukiyar jama’an jihar a kowani lokaci, ya nemi hadin kansu a kowani lokaci domin cimma nasarar kyautaya tsaro.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jos
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wace Illa GB WhatsApp Ke Da Shi?

Next Post

Mahmoud Abbas: Inganta Dangantakar Da Ke Tsakanin Kasarsa Da Sin Na Karfafa Gwiwar Falasdinawa Wajen Samun Ci Gaba

Related

Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

2 hours ago
Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe
Labarai

Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe

12 hours ago
An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja
Labarai

An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja

13 hours ago
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana
Labarai

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana

17 hours ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (I)
Labarai

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (I)

19 hours ago
Kano
Labarai

Zargin Kin Amincewar Kwankwaso Zuwa APC: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Mai Taimaka Ma Ta

20 hours ago
Next Post
Mahmoud Abbas: Inganta Dangantakar Da Ke Tsakanin Kasarsa Da Sin Na Karfafa Gwiwar Falasdinawa Wajen Samun Ci Gaba

Mahmoud Abbas: Inganta Dangantakar Da Ke Tsakanin Kasarsa Da Sin Na Karfafa Gwiwar Falasdinawa Wajen Samun Ci Gaba

LABARAI MASU NASABA

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

May 19, 2025
Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

May 19, 2025
Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)

Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)

May 18, 2025
Abin Da Ya Dace Ki Yi Yayin Haila Da Bayan Kin Gama?

Abin Da Ya Dace Ki Yi Yayin Haila Da Bayan Kin Gama?

May 18, 2025
Ciwon Mara Lokacin Al’ada

Ciwon Mara Lokacin Al’ada

May 18, 2025
Kasar Sin Ta Samu Bunkasar Masana’antar Harkokin Tauraron Dan Adam A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Bunkasar Masana’antar Harkokin Tauraron Dan Adam A Shekarar 2024

May 18, 2025
Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe

Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe

May 18, 2025
An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja

An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja

May 18, 2025
Kasar Sin Ta Sanya Harajin Takaita Shigo Da Kayayyakin Robobi Masu Tauri

Kasar Sin Ta Sanya Harajin Takaita Shigo Da Kayayyakin Robobi Masu Tauri

May 18, 2025
Yadda Ake Hada Danderun Kaza

Yadda Ake Hada Danderun Kaza

May 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.