• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daliban Shirin ‘N-Build’ Kashi Na ‘C1’ Sun Samu Horo Tare da Kayan Aiki

by Sulaiman
3 years ago
'N-Build'

Daliban shirin ‘N-Build’ kashi na ‘C1’ sun samu horo, tare da kayan aiki.

Ministar Harkokin Jinkai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta bayyana cewa horaswar da aka ba daliban shirin ‘N-Build’ kashi na ‘C1’ za ta amfane su a tsawon rayuwar su, kuma a duk inda su ka shiga.

Ministar ta bayyana haka ne a wajen bikin yaye daliban da su ka ci gajiyar shirin, kashi na ‘C1’, wanda aka yi a ranar Laraba a Abuja.

An yi watanni uku ana horas da waɗanda su ka shiga tsarin, wanda aka yi a karkashin shirin nan na Gwamnatin Tarayya na inganta rayuwar ‘yan Nijeriya, wato ‘National Social Investment Programme’ (NSIP) da kuma shirin ‘N-Power’.

A wajen bikin, ministar ta kuma raba kayan aiki ga dukkan wadanda aka yaye a wata makarantar koyar da sana’o’i mai suna ‘FOCI Skills Academy’ da ke unguwar Katampe a Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

A taron, Hajiya Sadiya ta yi la’akari da cewa wannan horaswa ko tirenin da aka yi, an yi irin sa a wasu cibiyoyi har 693 a faɗin kasar nan da nufin karfafa wa matasan da ba su da aikin yi gwiwa domin su samu kwarewar yin sana’a da za ta taimaki rayuwar su.

Ta ce masu, “Kwarewar da ku ka samu wajen horaswar a watanni uku da su ka gabata za ta kasance muhimmiyar hanyar da za ta taimake ku a yau da kuma gobe a kowane tsarin tattalin arziki na duniya.

“Wannan ma’aikata, tare da shugabannin gudanar da shirin NSIP da ‘N-Power’ da sauran cibiyoyin da abin ya shafa, sun yi aiki tukuru don tabbatar da cewa wannan abu ya taimaka wajen rage bukatar da ake yi ta kwararrun da aka horas don daukar su aiki.

“A wannan aji na ‘C1’ na shirin ‘N-Build’, an yaye dalibai ne domin su fara zama karkashin wasu masu irin sana’ar su, kamar yadda mai girma Shugaban Kasa ya Kudurci samar da karin ayyukan yi da hanyoyin samun arziki ga dimbin matasa. Za a tura su zuwa wurare daban-daban inda za su fara ayyukan su.

“Sannan su ma ‘yan aji na C2 na shirin ‘N-Power’, nan da makonni kaɗan za a tura su cibiyoyin horaswa, wanda duk manufar dai ita ce a tsamo ‘yan Nijeriya miliyan 100 daga ƙangin fatara.”

Ministar ta bayyana cewa an sama wa kowanne daga cikin masu cin moriyar shirin kunshin kayan aiki da kayan tsaron lafiyar jiki a wajen aiki, da kayan zuwa wajen horaswa don a ba su damar yin aiki a matsayin kwararrun masu sana’a da aka horas.

Ta yi kira a gare su da su yi amfani sosai da horaswar da aka ba su.

Hajiya Sadiya ta ce: “Tunda har kun gama horaswar cikin gida, za a hada ku kai-tsaye da hukumomin da su ka dace domin zaman koyo da za ku yi da su na tsawon wata shida.

“Wannan zaman koyon zai ba ku damar samun ilimin aiki, wanda za a fara shi daga ranar Litinin, 13 ga Yuni, 2022.

“A lokacin wannan zaman koyon na watanni shida, za a duba aikin ku tare da auna shi, wanda Cibiyar Magina ta Nijeriya Mai Rajista (Council of Registered Builders of Nigeria, CORBON) da Cibiyar Tsara Kayan Ƙirƙira ta Ƙasa (National Automotive Design and Development Council, NADDC) da kuma Hukumar Ƙwararru ta Masu Aikin Yawon Shaƙatawa ta Nijeriya (Institute of Tourism Professionals of Nigeria, ITPN) su za su yi maku.”

Ɗaliban da aka yaye ɗin dai sun samu horo ne a fagagen gyaran mota, fasahar aikin gona, aikin kafinta, aikin haɗa wutar lantarki, aikin gini da sa tayil, aikin famfo da shimfiɗa fayif.

Haka kuma ministar ta je Gidauniyar Cibiyar Masana’antu (Industrial Trust Fund Centre) domin miƙa ƙunshin kayan aiki da kayan fara sana’a ga ɗaliban da aka yaye a fagen sana’ar yawon buɗe ido, waɗanda su ka haɗa da koyon tuya da haɗa alawa, dafa abinci, kula da gida da kimtsa shi, da kuma dabarun haɗa abin sha.

Waɗanda su ka halarci taron sun haɗa da Mataimakin Shugaban Jami’ar Ahmadu Bello, Farfesa Kabiru Bala, da Darakta-Janar na Hukumar Magina ta Ƙasa (Federation of Construction Industry), Mista Olubunmi Adekoje, da Babban Kodineta na Shirin NSIP, Dakta Umar Bindir, da shugaban masu aiwatar da shirin ‘N-Power’, Mista Nsikak Okon, da sauran manyan baƙi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 
Manyan Labarai

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC
Manyan Labarai

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Next Post
Manoma Sun Koka Kan Hauhawar Farashin Takin Zamani

Manoma Sun Koka Kan Hauhawar Farashin Takin Zamani

LABARAI MASU NASABA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
'N-Build'

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.