• English
  • Business News
Saturday, August 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daliban Shirin ‘N-Build’ Kashi Na ‘C1’ Sun Samu Horo Tare da Kayan Aiki

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Daliban Shirin ‘N-Build’ Kashi Na ‘C1’ Sun Samu Horo Tare da Kayan Aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daliban shirin ‘N-Build’ kashi na ‘C1’ sun samu horo, tare da kayan aiki.

Ministar Harkokin Jinkai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta bayyana cewa horaswar da aka ba daliban shirin ‘N-Build’ kashi na ‘C1’ za ta amfane su a tsawon rayuwar su, kuma a duk inda su ka shiga.

Ministar ta bayyana haka ne a wajen bikin yaye daliban da su ka ci gajiyar shirin, kashi na ‘C1’, wanda aka yi a ranar Laraba a Abuja.

An yi watanni uku ana horas da waɗanda su ka shiga tsarin, wanda aka yi a karkashin shirin nan na Gwamnatin Tarayya na inganta rayuwar ‘yan Nijeriya, wato ‘National Social Investment Programme’ (NSIP) da kuma shirin ‘N-Power’.

A wajen bikin, ministar ta kuma raba kayan aiki ga dukkan wadanda aka yaye a wata makarantar koyar da sana’o’i mai suna ‘FOCI Skills Academy’ da ke unguwar Katampe a Abuja.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

A taron, Hajiya Sadiya ta yi la’akari da cewa wannan horaswa ko tirenin da aka yi, an yi irin sa a wasu cibiyoyi har 693 a faɗin kasar nan da nufin karfafa wa matasan da ba su da aikin yi gwiwa domin su samu kwarewar yin sana’a da za ta taimaki rayuwar su.

Ta ce masu, “Kwarewar da ku ka samu wajen horaswar a watanni uku da su ka gabata za ta kasance muhimmiyar hanyar da za ta taimake ku a yau da kuma gobe a kowane tsarin tattalin arziki na duniya.

“Wannan ma’aikata, tare da shugabannin gudanar da shirin NSIP da ‘N-Power’ da sauran cibiyoyin da abin ya shafa, sun yi aiki tukuru don tabbatar da cewa wannan abu ya taimaka wajen rage bukatar da ake yi ta kwararrun da aka horas don daukar su aiki.

“A wannan aji na ‘C1’ na shirin ‘N-Build’, an yaye dalibai ne domin su fara zama karkashin wasu masu irin sana’ar su, kamar yadda mai girma Shugaban Kasa ya Kudurci samar da karin ayyukan yi da hanyoyin samun arziki ga dimbin matasa. Za a tura su zuwa wurare daban-daban inda za su fara ayyukan su.

“Sannan su ma ‘yan aji na C2 na shirin ‘N-Power’, nan da makonni kaɗan za a tura su cibiyoyin horaswa, wanda duk manufar dai ita ce a tsamo ‘yan Nijeriya miliyan 100 daga ƙangin fatara.”

Ministar ta bayyana cewa an sama wa kowanne daga cikin masu cin moriyar shirin kunshin kayan aiki da kayan tsaron lafiyar jiki a wajen aiki, da kayan zuwa wajen horaswa don a ba su damar yin aiki a matsayin kwararrun masu sana’a da aka horas.

Ta yi kira a gare su da su yi amfani sosai da horaswar da aka ba su.

Hajiya Sadiya ta ce: “Tunda har kun gama horaswar cikin gida, za a hada ku kai-tsaye da hukumomin da su ka dace domin zaman koyo da za ku yi da su na tsawon wata shida.

“Wannan zaman koyon zai ba ku damar samun ilimin aiki, wanda za a fara shi daga ranar Litinin, 13 ga Yuni, 2022.

“A lokacin wannan zaman koyon na watanni shida, za a duba aikin ku tare da auna shi, wanda Cibiyar Magina ta Nijeriya Mai Rajista (Council of Registered Builders of Nigeria, CORBON) da Cibiyar Tsara Kayan Ƙirƙira ta Ƙasa (National Automotive Design and Development Council, NADDC) da kuma Hukumar Ƙwararru ta Masu Aikin Yawon Shaƙatawa ta Nijeriya (Institute of Tourism Professionals of Nigeria, ITPN) su za su yi maku.”

Ɗaliban da aka yaye ɗin dai sun samu horo ne a fagagen gyaran mota, fasahar aikin gona, aikin kafinta, aikin haɗa wutar lantarki, aikin gini da sa tayil, aikin famfo da shimfiɗa fayif.

Haka kuma ministar ta je Gidauniyar Cibiyar Masana’antu (Industrial Trust Fund Centre) domin miƙa ƙunshin kayan aiki da kayan fara sana’a ga ɗaliban da aka yaye a fagen sana’ar yawon buɗe ido, waɗanda su ka haɗa da koyon tuya da haɗa alawa, dafa abinci, kula da gida da kimtsa shi, da kuma dabarun haɗa abin sha.

Waɗanda su ka halarci taron sun haɗa da Mataimakin Shugaban Jami’ar Ahmadu Bello, Farfesa Kabiru Bala, da Darakta-Janar na Hukumar Magina ta Ƙasa (Federation of Construction Industry), Mista Olubunmi Adekoje, da Babban Kodineta na Shirin NSIP, Dakta Umar Bindir, da shugaban masu aiwatar da shirin ‘N-Power’, Mista Nsikak Okon, da sauran manyan baƙi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matashin Dan Wasa Gavi Ya Kafa Tarihi A Tawagar Sifaniya

Next Post

Manoma Sun Koka Kan Hauhawar Farashin Takin Zamani

Related

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa
Labarai

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

3 hours ago
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
Rahotonni

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

4 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Labarai

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

5 hours ago
Akwai Bukatar Samar Da Sauyin Zaman Lafiya Mai Dorewa A Duniya — Maryam Bukar
Labarai

Akwai Bukatar Samar Da Sauyin Zaman Lafiya Mai Dorewa A Duniya — Maryam Bukar

7 hours ago
UBEC Ta Kaddamar Da Makarantun Zamani 21 A Sassan Nijeriya
Labarai

UBEC Ta Kaddamar Da Makarantun Zamani 21 A Sassan Nijeriya

8 hours ago
Gwamnatin Katsina Za Ta Samu Kudaden Bunkasa Ilimi
Labarai

Tetfund Ta Samar Da Naira Biliyan 100 Don Inganta Ilimin Likitanci – Masari

9 hours ago
Next Post
Manoma Sun Koka Kan Hauhawar Farashin Takin Zamani

Manoma Sun Koka Kan Hauhawar Farashin Takin Zamani

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

August 15, 2025
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

August 15, 2025
Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

August 15, 2025
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

August 15, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

August 15, 2025
Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

August 15, 2025
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

August 15, 2025
Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

August 15, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

August 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

August 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.