ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalibi Ya Daba Wa Wasu Dalibai 2 Wuka A Kan Musun Kwallon Kafa A Bauchi

by Sadiq
3 years ago
Dalibi

Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta tabbatar da cafke wani dalibin makarantar sakandiren gwamnati ta Games Village a cikin birnin Bauchi bisa zarginsa da daba wa wasu dalibai biyu wuka a kan musu.

Daliban sun yi musu ne a kan kungiyoyin kwallon kafa da suke goyon baya.

  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Abiodun Ya Bukaci A Yi Wa Nijeriya Addu’a
  • Farashin Tikitin Jiragen Sama Ya Yi Tashin Gwauron-Zabi A Nijeriya 

Daya daga cikinsu ya fito da wuka ya daba wa sauran biyun, daya a kirji, daya a cinyarsa.

ADVERTISEMENT

Kakakin rundunar ’yan sandan Bauchi, SP Ahmed Wakili, ya ce; “A ranar Alhamis da misalin karfe 4:45 na yamma, rundunar ‘yan sandan da ke sintiri a kauyen Games Village, ta hangi gungun daliban makarantar sakandaren gwamnati da ke kauyen Games Village.

“Da aka gudanar da bincike, an gano cewa wani Usman Suleiman Jahun, wanda aka fi sani da Jan Gashi, dan shekara 18, dalibin SS3, ya hada baki da wasu biyu wadanda yanzu haka ake nemansu, suka kai wa abokinsu farma da muggan makamai.”

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

Ya kara da cewa jami’an ‘yan sandan sun garzaya da wadanda abin ya shafa zuwa asibitin Ganjuwa.

“Rundunar ta na kara zage damtse wajen cafke wadanda ake zargi da suka gudu.

“Kwamishinan ‘yan sanda, Umar Mamman Sanda, ya bayar da umarnin a mika lamarin zuwa hukumar SCID domin gudanar da bincike,” a cewarsa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

APC
Labarai

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

November 11, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP
Manyan Labarai

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
Next Post
An Sauya Wa Ka’aba Sabuwar Rigar Da Kudinta Ya Kai Dala $6.5m

An Sauya Wa Ka'aba Sabuwar Rigar Da Kudinta Ya Kai Dala $6.5m

LABARAI MASU NASABA

APC

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

November 11, 2025
An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

November 11, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.