• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Muke Son Mafi Karanci Albashi Ya Kai Miliyan 1 – Ajaero

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Dalilin Da Ya Sa Muke Son Mafi Karanci Albashi Ya Kai Miliyan 1 – Ajaero
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kungiyar kwadago na kasa (NLC), Joe Ajaero ya ce da yiyuwar bukatar karin albashi mafi karanci ya lunka har zuwa miliyan daya a kowace wata lura da matsalolin rayuwa da tsadar kayan bukatu da ake fuskanta.

A cewar NLC, muddin matsatsin tattalin arziki ya ci gaba da tafiya a haka, babu shakka bukatunta zai sa ta nemi a biya mafi karancin albashi zuwa miliyan 1 a kowace wata ga ma’aikata.

  • Sin Za Ta Kaddamar Da Gangamin Yayata Ci Gaban Mata
  • Tinubu Ya Gwangwaje ‘Yan Wasan Nijeriya Da Kyautar Filaye Da Gidaje Da Lambar MON Ta Kasa

A hirarsa da gidan talabijin na Arise a ranar Lahadi, shugaban NLC, Joe Ajaero, ya ce, hauhawar farashin kayayyakin masarufi da kuma karyewar darajar naira suna daga cikin dalilan da za su sanya kungiyar neman a biya albashi mafi karanci na miliyan 1.

Ya ce, “Wannan naira miliyan 1 din zai iya zama abun bukata muddin darajar naira ya ci gaba da karyewa. Matukar hauhawar rashin kayan bukatu suka ci gaba da tashi. Kungiyar Kwadago na tsayuwa ne bisa abubuwan da suke faruwa a cikin al’umma.

“Za ku tuna lokacin da muke tunanin naira 200,000, farashin canji ya kai zuwa naira 900. Amma yanzu da nake magana, farashin canji ya kai zuwa naira 1,400 koma fiye.

Labarai Masu Nasaba

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

“Wadannan batutuwan su ne suke kai ga neman bukatar da muke da su, sannan ya shafi harkokin rayuwa, inda rayuwa ta yi matsatsi. Mun sha fada cewa bukatunmu za su tafi ne daidai da farashin tsadar rayuwa.

“Za ku amince da ni cewa farashin buhun shinkafa ya haura naira 60,000 zuwa naira 70,000. Kayan abinci na neman gagaran mutane. Yanzu, shin za mu samu mafi karancin albashin da ba zai ishemu na sufuri? “Muna da dukkanin wadannan batutuwan. Kuma hakan ne zai kai ga Sanya gwamnatin tarayya dukufa wajen wadannan yarjejeniyar,” ya shaida.

Wannan bayanan na Ajaero ya janyo barazanar tsunduma yajin aiki. Inda gwamnatin tarayya da kungiyoyin kwadago na NLC da TUC suka shirya zaman tattaunawa domin baje batutuwan da suke akwai kan gargadin shiga yajin aikin kwanaki 14.

Kungiyoyin kwadagon sun zargi gwamnatin da yin kunnen uwar shegu da cimma yarjejeniyar da suka yi a baya.

Ya ce, “Sau daya tak a wata daya aka biya naira 35,000 ga ma’aikata.

Kuma, babu wani shaidar biyan wani ma’aikaci naira 25,000 a matsayin tallafi. Abun da ya haifar da abun da ke faruwa a ma’aikatar jin kai.

“Babu wani manomin da zai zo ya ce ya amshi taki daga wajen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dokar Hana Fitar Da Kayan Gini Waje: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Motoci 5 Makare Da Siminti A Adamawa

Next Post

Ƙungiyar Ƙwadago Za Ta Gudanar Da Zanga-zangar Nuna Adawa Da Tsadar Rayuwa 

Related

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

1 hour ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

13 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

18 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

19 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

20 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

21 hours ago
Next Post
NLC

Ƙungiyar Ƙwadago Za Ta Gudanar Da Zanga-zangar Nuna Adawa Da Tsadar Rayuwa 

LABARAI MASU NASABA

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.