• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Muke Son Mafi Karanci Albashi Ya Kai Miliyan 1 – Ajaero

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Albashi

Shugaban kungiyar kwadago na kasa (NLC), Joe Ajaero ya ce da yiyuwar bukatar karin albashi mafi karanci ya lunka har zuwa miliyan daya a kowace wata lura da matsalolin rayuwa da tsadar kayan bukatu da ake fuskanta.

A cewar NLC, muddin matsatsin tattalin arziki ya ci gaba da tafiya a haka, babu shakka bukatunta zai sa ta nemi a biya mafi karancin albashi zuwa miliyan 1 a kowace wata ga ma’aikata.

  • Sin Za Ta Kaddamar Da Gangamin Yayata Ci Gaban Mata
  • Tinubu Ya Gwangwaje ‘Yan Wasan Nijeriya Da Kyautar Filaye Da Gidaje Da Lambar MON Ta Kasa

A hirarsa da gidan talabijin na Arise a ranar Lahadi, shugaban NLC, Joe Ajaero, ya ce, hauhawar farashin kayayyakin masarufi da kuma karyewar darajar naira suna daga cikin dalilan da za su sanya kungiyar neman a biya albashi mafi karanci na miliyan 1.

Ya ce, “Wannan naira miliyan 1 din zai iya zama abun bukata muddin darajar naira ya ci gaba da karyewa. Matukar hauhawar rashin kayan bukatu suka ci gaba da tashi. Kungiyar Kwadago na tsayuwa ne bisa abubuwan da suke faruwa a cikin al’umma.

“Za ku tuna lokacin da muke tunanin naira 200,000, farashin canji ya kai zuwa naira 900. Amma yanzu da nake magana, farashin canji ya kai zuwa naira 1,400 koma fiye.

LABARAI MASU NASABA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

“Wadannan batutuwan su ne suke kai ga neman bukatar da muke da su, sannan ya shafi harkokin rayuwa, inda rayuwa ta yi matsatsi. Mun sha fada cewa bukatunmu za su tafi ne daidai da farashin tsadar rayuwa.

“Za ku amince da ni cewa farashin buhun shinkafa ya haura naira 60,000 zuwa naira 70,000. Kayan abinci na neman gagaran mutane. Yanzu, shin za mu samu mafi karancin albashin da ba zai ishemu na sufuri? “Muna da dukkanin wadannan batutuwan. Kuma hakan ne zai kai ga Sanya gwamnatin tarayya dukufa wajen wadannan yarjejeniyar,” ya shaida.

Wannan bayanan na Ajaero ya janyo barazanar tsunduma yajin aiki. Inda gwamnatin tarayya da kungiyoyin kwadago na NLC da TUC suka shirya zaman tattaunawa domin baje batutuwan da suke akwai kan gargadin shiga yajin aikin kwanaki 14.

Kungiyoyin kwadagon sun zargi gwamnatin da yin kunnen uwar shegu da cimma yarjejeniyar da suka yi a baya.

Ya ce, “Sau daya tak a wata daya aka biya naira 35,000 ga ma’aikata.

Kuma, babu wani shaidar biyan wani ma’aikaci naira 25,000 a matsayin tallafi. Abun da ya haifar da abun da ke faruwa a ma’aikatar jin kai.

“Babu wani manomin da zai zo ya ce ya amshi taki daga wajen.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma
Labarai

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Next Post
NLC

Ƙungiyar Ƙwadago Za Ta Gudanar Da Zanga-zangar Nuna Adawa Da Tsadar Rayuwa 

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.