ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Muke Son Mafi Karanci Albashi Ya Kai Miliyan 1 – Ajaero

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Albashi

Shugaban kungiyar kwadago na kasa (NLC), Joe Ajaero ya ce da yiyuwar bukatar karin albashi mafi karanci ya lunka har zuwa miliyan daya a kowace wata lura da matsalolin rayuwa da tsadar kayan bukatu da ake fuskanta.

A cewar NLC, muddin matsatsin tattalin arziki ya ci gaba da tafiya a haka, babu shakka bukatunta zai sa ta nemi a biya mafi karancin albashi zuwa miliyan 1 a kowace wata ga ma’aikata.

  • Sin Za Ta Kaddamar Da Gangamin Yayata Ci Gaban Mata
  • Tinubu Ya Gwangwaje ‘Yan Wasan Nijeriya Da Kyautar Filaye Da Gidaje Da Lambar MON Ta Kasa

A hirarsa da gidan talabijin na Arise a ranar Lahadi, shugaban NLC, Joe Ajaero, ya ce, hauhawar farashin kayayyakin masarufi da kuma karyewar darajar naira suna daga cikin dalilan da za su sanya kungiyar neman a biya albashi mafi karanci na miliyan 1.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Wannan naira miliyan 1 din zai iya zama abun bukata muddin darajar naira ya ci gaba da karyewa. Matukar hauhawar rashin kayan bukatu suka ci gaba da tashi. Kungiyar Kwadago na tsayuwa ne bisa abubuwan da suke faruwa a cikin al’umma.

“Za ku tuna lokacin da muke tunanin naira 200,000, farashin canji ya kai zuwa naira 900. Amma yanzu da nake magana, farashin canji ya kai zuwa naira 1,400 koma fiye.

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

“Wadannan batutuwan su ne suke kai ga neman bukatar da muke da su, sannan ya shafi harkokin rayuwa, inda rayuwa ta yi matsatsi. Mun sha fada cewa bukatunmu za su tafi ne daidai da farashin tsadar rayuwa.

“Za ku amince da ni cewa farashin buhun shinkafa ya haura naira 60,000 zuwa naira 70,000. Kayan abinci na neman gagaran mutane. Yanzu, shin za mu samu mafi karancin albashin da ba zai ishemu na sufuri? “Muna da dukkanin wadannan batutuwan. Kuma hakan ne zai kai ga Sanya gwamnatin tarayya dukufa wajen wadannan yarjejeniyar,” ya shaida.

Wannan bayanan na Ajaero ya janyo barazanar tsunduma yajin aiki. Inda gwamnatin tarayya da kungiyoyin kwadago na NLC da TUC suka shirya zaman tattaunawa domin baje batutuwan da suke akwai kan gargadin shiga yajin aikin kwanaki 14.

Kungiyoyin kwadagon sun zargi gwamnatin da yin kunnen uwar shegu da cimma yarjejeniyar da suka yi a baya.

Ya ce, “Sau daya tak a wata daya aka biya naira 35,000 ga ma’aikata.

Kuma, babu wani shaidar biyan wani ma’aikaci naira 25,000 a matsayin tallafi. Abun da ya haifar da abun da ke faruwa a ma’aikatar jin kai.

“Babu wani manomin da zai zo ya ce ya amshi taki daga wajen.

Albashi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Labarai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
'yansanda
Labarai

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Next Post
NLC

Ƙungiyar Ƙwadago Za Ta Gudanar Da Zanga-zangar Nuna Adawa Da Tsadar Rayuwa 

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.