Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta bayyana dalilin da ya sa sauran sanatoci ba su mara mata goyon baya ba lokacin da aka dakatar da ita na tsawon watanni shida a Majalisar Dattawa.
Yayin buɗe sabuwar kasuwa a garin Okene, Jihar Kogi, Natasha ta ce yawancin sanatoci sun ji tsoron zaluncin siyasa idan suka goyo maga baya a bainar jama’a.
- Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin
 - “Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan Trump
 
Ta bayyana cewa wasu daga cikin abokan aikinta sun kira ta da kansu sun kuma tausaya mata tare da goyon bayanta, amma sun guji yin hakan a fili saboda tsoron hukunci ko tsangwama.
“Idan jami’in gwamnati ya shiga matsala, mutane kan rabu da shi,” in ji ta.
“Da dama daga cikin sanatoci sun goyi bayana a sirrance, sun kira ni, wasu ma sun zo sun ganni amma ba su iya nuna hakan a bainar jama’a ba. Ban ji haushi ba.”
Natasha ta bayyana dakatar da ita a matsayin mataki wanda ba na doka ba, tana mai cewa hakan ya nuna yadda tsoro da barazanar siyasa ke rinjayar halayen jami’an gwamnati.
An dakatar da Sanata Natasha a watan Maris saboda zargin da ya shafi Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, amma ta koma kujerarta a watan Satumba bayan kammala wa’adin dakatarwar.
			




							








