• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Haramta Tafiyar Dare A Iyakokinmu Da Katsina Da Sokoto – Gwamnatin Zamfara

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara ta yanke shawarar haramta zirga-zirga daga karfe 7:00 na dare zuwa karfe 6:00 na safe a kan iyakokin jihar da makwaftanta, Jihohin Katsina da Sakkwato.

Kwamishinan Yada Labarai da Al’adu na Jihar, Manir Haidar ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Gusau ranar Talata.
Haidara ya ce an yanke wannan shawarar ne a yayin taron kwamitin tsaro na jihar.

  • Hisba Ta Cafke Mata 7 Da Ake Zargi Da Satar Yadidduka A Kano
  • Jihar Zamfara Ta Haramta Zirga-zirga A Tsakanin Iyakokinta Da Katsina Da Sokoto Daga Karfe 7 Na Yamma

Ya ce, “Ya zuwa yau (ranar Talata), gwamnatin jihar ta ba da umarnin hana zirga-zirga a kan iyakar Yankara da Jihar Zamfara da Jihar Katsina da kuma kan iyakar Bimasa Zamfara da Jihar Sokoto daga karfe 7:00 na safe. zuwa 6:00 na safe kullum.

“An yi hakan ne don magance matsalar sace-sacen matafiya a kan babbar hanyar Sakkwato zuwa Gusau-Funtua.”

“Wannan wani bangare ne na matakan da gwamnatin jihar ke dauka na ragewa tare da magance ayyukan sace-sacen da ‘yan bindiga ke yi, musamman a manyan titunan jihar,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

A cewar kwamishinan, an umurci dukkan masu ababen hawa da matafiya da su bi umarnin gwamnati.

“An umurci hukumomin tsaro da su sanya ido kan iyakokin biyu tare da tabbatar da cikakkiyar kulawa,” in ji shi.

…’Yan Bindiga Sun Sace Masu Sallar Tahajjud

A wani labarin kuma, a daren Litinin din da ta gabata, wasu ‘yan bindiga sun kai hari a wani masallaci da ke Gusau, Babban Birnin Jihar Zamfara, inda suka yi awon gaba da wasu masu ibada a lokacin da suke Sallar Tahajjud.

Sallar Tahajjud ibada ce da aka saba gudanarwa a cikin kwanaki 10 na karshen watan Ramadan gabanin ranar karamar sallah.

A cewar wani mazaunin unguwar mai suna Mannir wanda ya zanta da LEADERSHIP, maharan sun far wa masallacin ne a lokacin da ake Sallar dare.

Mannir, ya bayyana rashin tabbas game da ainihin adadin mutanen da aka kama.
Mannir ya kara da cewa “Yayin da har yanzu ba a tabbatar da adadin wadanda aka sace ba, hukumomi na ci gaba da bibiyar maharan.”

Har ya zuwa lokacin da aka fitar da wannan rahoto, babu wata kungiya da ta dauki alhakin kai wannan kazamin hari, lamarin da ya kara janyo rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma.

Wannan harin na zuwa ne a daidai lokacin da ake fargabar karuwar ta’addanci da ayyukan ta’addanci a Jihar Zamfara. Idan dai za a iya tunawa, a mako guda da ya gabata ne Gwamna Dauda Lawal ya tattauna da Shugaban Kasa Bola Tinubu domin shawo kan matsalolin tsaro da ke kara kamari a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Next Post
Eid-el-fitr: Gwamnatin Tarayya Ta Tsawaita Hutun Bukukuwan Sallah 

Eid-el-fitr: Gwamnatin Tarayya Ta Tsawaita Hutun Bukukuwan Sallah 

LABARAI MASU NASABA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025
Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

October 31, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.