ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Karuwar Garkuwa Da Mutane Duk Da Hada Layukan Waya Da Lambar NIN – Pantami

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Pantami

Tsohon ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani, Farfesa Isa Pantami, ya ce, rashin rungumar tsarin hada layukan waya da lambar shaidar dan kasa (NIN-SIM) ya bai wa ayyukan ta’addancin kwarin guiwar ci gaba da tsula tsiya, musamman garkuwa da mutane a fadin kasar nan.

Ministan wanda ke ba da amsa kam tambayar da wani ya yi a shafin Tiwuta mai suna Mentus da ya yi tambayar me ya sa aka tursasa ‘yan Nijeriya zuwa hada lambar wayarsu da lambar NIM da nufin dakile ayyukan ta’addanci amma har yanzu ayyukan ta’addancin na ci gaba da wakana.

  • NIS Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”
  • ‘Yansanda Sun Cafke Wasu Mutane Biyu Da Ake Zargi Da Satar Keke-napep A Kano

Mai tambayar ya ce me ya sa aka sanya ‘yan Nijeriya mallakar shaidar NIN? Da ba a tilasta musu ba in an san ba zai yi tasiri ba.

ADVERTISEMENT

Tun da farko, tsohon ministan ya wallafa cewa daya daga cikin abokansa ya tara naira miliyan hamsin a matsayin gudunmawar da aka harhada domin tara naira miliyan 100 da masu garkuwa da mutane suka bukata bayan sace ‘yan mata shida a Abuja.

Ya ce, ya yi magana da mahaifin ‘yan matan biyo bayan kashe daya daga cikinsu Najeeba wacce take gab da kammala jami’a biyo bayan gaza biyan kudin fansar da mahaifin nasu ya kasa yi na biyan miliyan 60.

LABARAI MASU NASABA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Pantami wanda shi ne ya kawo tsarin hada lambar NIN-SIM ya ce, kwata-kwata ba tsarin ne ke da matsala ba, illa rashin tabbatar da amfani da tsari da hukumomi da cibiyoyi suka kasa yi shi ne babban matsalar.

Ya daura alhalin rashin amfanin tsarin ga hukumomin da aka ware domin kare rayukan al’umma, inda suka yi watsi da hakan duk kuwa da cewa suna da kayan aikin da suka dace na bibiya da bin sawun masu amfani da layukan wayoyi.

“Tsarin NIN-SIM na aiki sosai. Amma, hukumomin da abun ya shafa da ke yaki da ‘yan ta’addan an bukaci su tabbatar da amfani da tsari a duk lokacin da aka aikata wani ta’addanci. Amma rashin amfani da tsarin da aiwatar da shi shi ne babban matsalar ba wai tsarin ba.

“Idan har hukumomin da suka dace ba su yi amfani da tsarin ba wajen kare rayuka da dukiyar jama’an kowani mutum to da matsala, ni na sadaukar da rayuwana na kau da kaina daga dukkanin barazanar kasheni domin tabbatar da fito da wannan tsarin,” ya shaida.

Pantami
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
Rahotonni

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
Labarai

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
Labarai

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
Next Post
Fifikon Annabi (SAW) Da Na Al’ummarsa

Fifikon Annabi (SAW) Da Na Al’ummarsa

LABARAI MASU NASABA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.