• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Karuwar Garkuwa Da Mutane Duk Da Hada Layukan Waya Da Lambar NIN – Pantami

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Dalilin Karuwar Garkuwa Da Mutane Duk Da Hada Layukan Waya Da Lambar NIN – Pantami
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani, Farfesa Isa Pantami, ya ce, rashin rungumar tsarin hada layukan waya da lambar shaidar dan kasa (NIN-SIM) ya bai wa ayyukan ta’addancin kwarin guiwar ci gaba da tsula tsiya, musamman garkuwa da mutane a fadin kasar nan.

Ministan wanda ke ba da amsa kam tambayar da wani ya yi a shafin Tiwuta mai suna Mentus da ya yi tambayar me ya sa aka tursasa ‘yan Nijeriya zuwa hada lambar wayarsu da lambar NIM da nufin dakile ayyukan ta’addanci amma har yanzu ayyukan ta’addancin na ci gaba da wakana.

  • NIS Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”
  • ‘Yansanda Sun Cafke Wasu Mutane Biyu Da Ake Zargi Da Satar Keke-napep A Kano

Mai tambayar ya ce me ya sa aka sanya ‘yan Nijeriya mallakar shaidar NIN? Da ba a tilasta musu ba in an san ba zai yi tasiri ba.

Tun da farko, tsohon ministan ya wallafa cewa daya daga cikin abokansa ya tara naira miliyan hamsin a matsayin gudunmawar da aka harhada domin tara naira miliyan 100 da masu garkuwa da mutane suka bukata bayan sace ‘yan mata shida a Abuja.

Ya ce, ya yi magana da mahaifin ‘yan matan biyo bayan kashe daya daga cikinsu Najeeba wacce take gab da kammala jami’a biyo bayan gaza biyan kudin fansar da mahaifin nasu ya kasa yi na biyan miliyan 60.

Labarai Masu Nasaba

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Pantami wanda shi ne ya kawo tsarin hada lambar NIN-SIM ya ce, kwata-kwata ba tsarin ne ke da matsala ba, illa rashin tabbatar da amfani da tsari da hukumomi da cibiyoyi suka kasa yi shi ne babban matsalar.

Ya daura alhalin rashin amfanin tsarin ga hukumomin da aka ware domin kare rayukan al’umma, inda suka yi watsi da hakan duk kuwa da cewa suna da kayan aikin da suka dace na bibiya da bin sawun masu amfani da layukan wayoyi.

“Tsarin NIN-SIM na aiki sosai. Amma, hukumomin da abun ya shafa da ke yaki da ‘yan ta’addan an bukaci su tabbatar da amfani da tsari a duk lokacin da aka aikata wani ta’addanci. Amma rashin amfani da tsarin da aiwatar da shi shi ne babban matsalar ba wai tsarin ba.

“Idan har hukumomin da suka dace ba su yi amfani da tsarin ba wajen kare rayuka da dukiyar jama’an kowani mutum to da matsala, ni na sadaukar da rayuwana na kau da kaina daga dukkanin barazanar kasheni domin tabbatar da fito da wannan tsarin,” ya shaida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Garkuwa Da Mutane Na Kara Ta’azzara A Nijeriya

Next Post

Fifikon Annabi (SAW) Da Na Al’ummarsa

Related

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

2 hours ago
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Manyan Labarai

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

3 hours ago
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820
Manyan Labarai

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

5 hours ago
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki
Manyan Labarai

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

6 hours ago
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

14 hours ago
Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo
Manyan Labarai

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

16 hours ago
Next Post
Fifikon Annabi (SAW) Da Na Al’ummarsa

Fifikon Annabi (SAW) Da Na Al’ummarsa

LABARAI MASU NASABA

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.