• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilinmu Na Yi Wa ASUU Kishiya –Gwamnati

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Dalilinmu Na Yi Wa ASUU Kishiya –Gwamnati

Chris Ngige

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta yi wa sababbin kungiyoyin jami’o’in Nijeriya guda biyu rajista a hukumance a matsayin kungiyoyin kasuwanci.

Wadanda suke kusa da lamarin sun bayyana cewa sababbin kungiyoyin sun kasance kishiyoyi ga kungiyar malaman jami’a’o’i ta kasa (ASUU), wadda da dage tana jayayya da gwamnatin tarayya.

  • Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe
  • Gwamnatin Habasha Da ‘Yan Tawayen Tigray Za Su Zauna A Teburin Sulhu

Sababbin kungiyoyin da aka yi wa rajista dai sun hada da ‘Congressof Nigerian Unibersity Academics (CONUA), da ‘Nigeria Associationof Medical and Dental Lecturers in Academics (NAMDA).’

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan gabatar da takardar yi wa kungiyoyin guda biyu rajista a Abuja, Ministan kwadugo da samar da ayyukan yi, Chris Ngige, ya bayyana cewa wannan mataki yana kan tsarin dokar kasa domin shawo kan matsalolin da jami’o’in suke fuskanta.

Ngige ya kara da cewa wadannan kungiyoyi guda biyu wani bangare nena ASUU da suka balle daga jami’o’in Nijeriya, kamar yadda dokar kasa da kasa na kafa kungiyoyin mai lamba 87 da 98 ta tanada, wanda ya bai wa kungiyoyin ‘yancin kare hakkinsu.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Ngige ya ce, “Ma’aikatar kwadugo da samar da ayyukan yi ta yi gaban kanta wajen fito da sababbin kungiyoyin kasuwanci domin habaka tsarin kasuwanci a cikin kasar nan tare da yanke shawarar amincewa da yi wa sabbin kungiyoyi guda biyu rajista a karkashin jami’o’in Nijeriya.

“Watanni 8 da suka gabata, jami’o’in gwamnatin tarayya suna rufe, sannan dalibai suna zaune a gida sakamakon yajin aiki da kungiyar ASUU suke yi, duk da kokarin sasantawa da gwamnatin tarayya ta yi, amma lamarin ya ci tura.

“Karkashin dokar kasuwanci na gwamnatin tarayya ta shekarar 2004,wannan yajin aiki ya kamata ya kawo karshe tun a zaman sulhu da wannan ma’aikata da yi kokarin yi a ranakun 22 ga watan Fabrairun 2022 da ranar 1 ga watan Maris ta 2022.

“Duk wani kokarin sulhu ya ci tura, sakamakon dagewa da kungiyar ASUU ta yi wanda har kotun da’ar ma’aikata ta zantar da hukunci a matsayinta da take sasanta rikici a tsakanin kungiyoyi, amma ASUU ta ki bin wannan umarni.

“Abun ban sha’awar dai shi ne, mafi yawancin malaman jami’o’in da ke karantarwa a makarantun gwamnati sun nuna sha’awarsu na komawa bakin aiki idan aka sulhunta,” Ngige.

A nasa martanin, shugaban kungiyar ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ya bayyana cewa sababbin kungiyoyin da aka yi wa rajista ba mambobinsu ba ne, ya dai zargi gwamnatin tarayya da yin farfaganda wajen kare laifinta a wurin ‘yan Nijeriya.

Ya kara da cewa gwamnatin tarayya tana yin dukkkan wadannan abubuwa ne saboda mambobin ASUU sun ki rakonta kan tsayar musu da albashinsu.

Hakazalika, shugaban majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila ya bayyana cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari shi ne mai wuka da nama na yanke hukunci na karshe kan yajin aikin ASUU bayan ganawarsa da zauran majalisar wakilai a wannan mako.

Ya dai bayyana hakan ne jim kadan bayan kammala zaman ganawar sulhu tsakanin shugaban kasa da ‘yan majalisar a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Shugaban majalisar wakilan yana fatan za a samu sulhu bayan gabatar da rahoto, inda ya roki shugabankasa ya yi nazari a rahoton kafin su sake zama da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ASUUBuhariChris NgigeDalibaiGwamnatin TarayyaKungiyoyiMa'aikataYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Daukaka Kara Ta Umurci Kungiyar ASUU Da Ta Gaggauta Janye Yajin Aikin Da Take

Next Post

Yadda Ta Kaya A Taron Gwamnonin Nijeriya Da Nijer A Katsina

Related

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

1 hour ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

16 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

17 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

19 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

20 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

21 hours ago
Next Post
Yadda Ta Kaya A Taron Gwamnonin Nijeriya Da Nijer A Katsina

Yadda Ta Kaya A Taron Gwamnonin Nijeriya Da Nijer A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.