• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilinmu Na Yi Wa ASUU Kishiya –Gwamnati

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Dalilinmu Na Yi Wa ASUU Kishiya –Gwamnati

Chris Ngige

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta yi wa sababbin kungiyoyin jami’o’in Nijeriya guda biyu rajista a hukumance a matsayin kungiyoyin kasuwanci.

Wadanda suke kusa da lamarin sun bayyana cewa sababbin kungiyoyin sun kasance kishiyoyi ga kungiyar malaman jami’a’o’i ta kasa (ASUU), wadda da dage tana jayayya da gwamnatin tarayya.

  • Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe
  • Gwamnatin Habasha Da ‘Yan Tawayen Tigray Za Su Zauna A Teburin Sulhu

Sababbin kungiyoyin da aka yi wa rajista dai sun hada da ‘Congressof Nigerian Unibersity Academics (CONUA), da ‘Nigeria Associationof Medical and Dental Lecturers in Academics (NAMDA).’

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan gabatar da takardar yi wa kungiyoyin guda biyu rajista a Abuja, Ministan kwadugo da samar da ayyukan yi, Chris Ngige, ya bayyana cewa wannan mataki yana kan tsarin dokar kasa domin shawo kan matsalolin da jami’o’in suke fuskanta.

Ngige ya kara da cewa wadannan kungiyoyi guda biyu wani bangare nena ASUU da suka balle daga jami’o’in Nijeriya, kamar yadda dokar kasa da kasa na kafa kungiyoyin mai lamba 87 da 98 ta tanada, wanda ya bai wa kungiyoyin ‘yancin kare hakkinsu.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Ngige ya ce, “Ma’aikatar kwadugo da samar da ayyukan yi ta yi gaban kanta wajen fito da sababbin kungiyoyin kasuwanci domin habaka tsarin kasuwanci a cikin kasar nan tare da yanke shawarar amincewa da yi wa sabbin kungiyoyi guda biyu rajista a karkashin jami’o’in Nijeriya.

“Watanni 8 da suka gabata, jami’o’in gwamnatin tarayya suna rufe, sannan dalibai suna zaune a gida sakamakon yajin aiki da kungiyar ASUU suke yi, duk da kokarin sasantawa da gwamnatin tarayya ta yi, amma lamarin ya ci tura.

“Karkashin dokar kasuwanci na gwamnatin tarayya ta shekarar 2004,wannan yajin aiki ya kamata ya kawo karshe tun a zaman sulhu da wannan ma’aikata da yi kokarin yi a ranakun 22 ga watan Fabrairun 2022 da ranar 1 ga watan Maris ta 2022.

“Duk wani kokarin sulhu ya ci tura, sakamakon dagewa da kungiyar ASUU ta yi wanda har kotun da’ar ma’aikata ta zantar da hukunci a matsayinta da take sasanta rikici a tsakanin kungiyoyi, amma ASUU ta ki bin wannan umarni.

“Abun ban sha’awar dai shi ne, mafi yawancin malaman jami’o’in da ke karantarwa a makarantun gwamnati sun nuna sha’awarsu na komawa bakin aiki idan aka sulhunta,” Ngige.

A nasa martanin, shugaban kungiyar ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ya bayyana cewa sababbin kungiyoyin da aka yi wa rajista ba mambobinsu ba ne, ya dai zargi gwamnatin tarayya da yin farfaganda wajen kare laifinta a wurin ‘yan Nijeriya.

Ya kara da cewa gwamnatin tarayya tana yin dukkkan wadannan abubuwa ne saboda mambobin ASUU sun ki rakonta kan tsayar musu da albashinsu.

Hakazalika, shugaban majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila ya bayyana cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari shi ne mai wuka da nama na yanke hukunci na karshe kan yajin aikin ASUU bayan ganawarsa da zauran majalisar wakilai a wannan mako.

Ya dai bayyana hakan ne jim kadan bayan kammala zaman ganawar sulhu tsakanin shugaban kasa da ‘yan majalisar a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Shugaban majalisar wakilan yana fatan za a samu sulhu bayan gabatar da rahoto, inda ya roki shugabankasa ya yi nazari a rahoton kafin su sake zama da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ASUUBuhariChris NgigeDalibaiGwamnatin TarayyaKungiyoyiMa'aikataYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Daukaka Kara Ta Umurci Kungiyar ASUU Da Ta Gaggauta Janye Yajin Aikin Da Take

Next Post

Yadda Ta Kaya A Taron Gwamnonin Nijeriya Da Nijer A Katsina

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

6 minutes ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

17 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Yadda Ta Kaya A Taron Gwamnonin Nijeriya Da Nijer A Katsina

Yadda Ta Kaya A Taron Gwamnonin Nijeriya Da Nijer A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.