ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilinmu Na Yi Wa ASUU Kishiya –Gwamnati

by Abdullahi Muh'd Sheka
4 years ago
Chris Ngige

Chris Ngige

Gwamnatin tarayya ta yi wa sababbin kungiyoyin jami’o’in Nijeriya guda biyu rajista a hukumance a matsayin kungiyoyin kasuwanci.

Wadanda suke kusa da lamarin sun bayyana cewa sababbin kungiyoyin sun kasance kishiyoyi ga kungiyar malaman jami’a’o’i ta kasa (ASUU), wadda da dage tana jayayya da gwamnatin tarayya.

  • Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe
  • Gwamnatin Habasha Da ‘Yan Tawayen Tigray Za Su Zauna A Teburin Sulhu

Sababbin kungiyoyin da aka yi wa rajista dai sun hada da ‘Congressof Nigerian Unibersity Academics (CONUA), da ‘Nigeria Associationof Medical and Dental Lecturers in Academics (NAMDA).’

ADVERTISEMENT

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan gabatar da takardar yi wa kungiyoyin guda biyu rajista a Abuja, Ministan kwadugo da samar da ayyukan yi, Chris Ngige, ya bayyana cewa wannan mataki yana kan tsarin dokar kasa domin shawo kan matsalolin da jami’o’in suke fuskanta.

Ngige ya kara da cewa wadannan kungiyoyi guda biyu wani bangare nena ASUU da suka balle daga jami’o’in Nijeriya, kamar yadda dokar kasa da kasa na kafa kungiyoyin mai lamba 87 da 98 ta tanada, wanda ya bai wa kungiyoyin ‘yancin kare hakkinsu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ngige ya ce, “Ma’aikatar kwadugo da samar da ayyukan yi ta yi gaban kanta wajen fito da sababbin kungiyoyin kasuwanci domin habaka tsarin kasuwanci a cikin kasar nan tare da yanke shawarar amincewa da yi wa sabbin kungiyoyi guda biyu rajista a karkashin jami’o’in Nijeriya.

“Watanni 8 da suka gabata, jami’o’in gwamnatin tarayya suna rufe, sannan dalibai suna zaune a gida sakamakon yajin aiki da kungiyar ASUU suke yi, duk da kokarin sasantawa da gwamnatin tarayya ta yi, amma lamarin ya ci tura.

“Karkashin dokar kasuwanci na gwamnatin tarayya ta shekarar 2004,wannan yajin aiki ya kamata ya kawo karshe tun a zaman sulhu da wannan ma’aikata da yi kokarin yi a ranakun 22 ga watan Fabrairun 2022 da ranar 1 ga watan Maris ta 2022.

“Duk wani kokarin sulhu ya ci tura, sakamakon dagewa da kungiyar ASUU ta yi wanda har kotun da’ar ma’aikata ta zantar da hukunci a matsayinta da take sasanta rikici a tsakanin kungiyoyi, amma ASUU ta ki bin wannan umarni.

“Abun ban sha’awar dai shi ne, mafi yawancin malaman jami’o’in da ke karantarwa a makarantun gwamnati sun nuna sha’awarsu na komawa bakin aiki idan aka sulhunta,” Ngige.

A nasa martanin, shugaban kungiyar ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ya bayyana cewa sababbin kungiyoyin da aka yi wa rajista ba mambobinsu ba ne, ya dai zargi gwamnatin tarayya da yin farfaganda wajen kare laifinta a wurin ‘yan Nijeriya.

Ya kara da cewa gwamnatin tarayya tana yin dukkkan wadannan abubuwa ne saboda mambobin ASUU sun ki rakonta kan tsayar musu da albashinsu.

Hakazalika, shugaban majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila ya bayyana cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari shi ne mai wuka da nama na yanke hukunci na karshe kan yajin aikin ASUU bayan ganawarsa da zauran majalisar wakilai a wannan mako.

Ya dai bayyana hakan ne jim kadan bayan kammala zaman ganawar sulhu tsakanin shugaban kasa da ‘yan majalisar a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Shugaban majalisar wakilan yana fatan za a samu sulhu bayan gabatar da rahoto, inda ya roki shugabankasa ya yi nazari a rahoton kafin su sake zama da shi.

ASUU
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
Next Post
Yadda Ta Kaya A Taron Gwamnonin Nijeriya Da Nijer A Katsina

Yadda Ta Kaya A Taron Gwamnonin Nijeriya Da Nijer A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.