• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangantaka Ta Yi Tsami Tsakanin Kwankwaso Da Shekarau

by Muhammad
3 years ago
Kwankwaso

Akwai alamun tsohon Gwamnan Jihar Kano, Ibrahim Shekarau, zai bayyana ficewarsa daga jam’iyyar NNPP ta Rabi’u Kwankwaso zuwa Jam’iyyar PDP, bayan samun wani sabani da gaza cika wasu alkawura daga bangaren Jagoran Jam’iyyar na kasa kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Rabi’u Kwankwaso.

Mai magana da yawun Sanata Shekarau, Malam Sule Ya’u Sule ya tabbatarwa da kafar yada labarai ta BBC Hausa cewa shakka babu an gaza cika alkawarin da kulla tunda farko tsakanin maigidan nasa da Kwankwaso gabanin shigarsu Jam’iyyar NNPP.

  • Babu Wanda Zai Fice Daga NNPP Da Zai Girgiza Siyasar Kwankwaso – Kofa

A gefe guda kuwa an jiyo Jagoran Ja’iyyar Sanata Kwankwaso na ikirarin cewa shi dai babu wani sabanin siyasa tsakaninsa da Sanata Shekarau a Jam’iyyar ta NNPP.

Da yake karin haske kan batun da ke yawo a kafafen yada labarai na hana Shekarau wasu kujerun takara ya ba mutanensa sai Kwankwason ya kayar da baki ya ce Shekarau din ya bayar da sunayen mutanen nasa a kure saboda lokacin da hukumar zabe ta bayar na sauya ‘yan takara ya kure.

Malam Shekarau, shi ne ke wakiltar mazabar Sanatan Kano ta tsakiya a majalisar dattawa, ya fice daga jam’iyyar APC zuwa NNPP a hukumance a wata wasika da shugaban majalisar, Ahmad Lawan ya karanta a zaman majalisar a ranar 29 ga watan Yuni.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

Wasu rahotanni na bayyana cewa, Sanata Shekarau din na ganawa da dan takarar shugaban kasa na PDP, Atiku Abubakar da abokin takararsa Ifeanyi Okowa da da Shugaban jam’iyyar na kasa, Iyochia Ayu, don ganin tsohon gwamnan ya koma Jam’iyyar PDP.

A ranar Lahadin da ta gabata ma, Shekarau ya kira wani taron gaggawa na majalisar shura kan harkokin siyasarsa tare da sanar da ƴan majalisar halin da ake ciki.

Idan hai ya yi zamu ci gaba da bibiyar wainar da ake toyawa tsakanin tsagin manyan jagororin siyasar Kanon don jin yadda zata kaya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Cimma Manyan Nasarori A Fannin Gina Intanet A Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Kasar Sin Ta Cimma Manyan Nasarori A Fannin Gina Intanet A Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

LABARAI MASU NASABA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.